< Zakariya 3 >

1 Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
And he showed me Joshua, the high-priest, standing before the angel of Jehovah, and the adversary standing at his right hand, to accuse him.
2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
And Jehovah said to the adversary: — Jehovah rebuke thee, thou adversary, Even Jehovah, who hath chosen Jerusalem, rebuke thee! Is not this man a brand plucked out of the fire?
3 Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
Now Joshua was clothed with filthy garments, and stood before the angel.
4 Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
And he [[the angel]] spake and said to them [[the angels]] that stood before him, saying, Take off the filthy garments from him. And to him he said, Behold, I have caused thine iniquity to pass from thee, and will clothe thee with goodly apparel.
5 Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
And I said, Let them set a fair mitre upon his head! And they set a fair mitre upon his head, and clothed him with garments. And the angel of Jehovah stood by.
6 Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
And the angel of Jehovah declared to Joshua and said:
7 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
Thus saith Jehovah of hosts: If thou wilt walk in my ways, And if thou wilt keep my charge, Then thou shalt also rule my house, And shalt also keep my courts, And I will give thee guides among these that stand by.
8 “‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
Hear now, O Joshua, high-priest, Thou and thy companions, who sit before thee! For they are men that are signs. For, behold, I will cause to come my servant, the Branch.
9 Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
For, behold, the stone which I have laid before Joshua, Upon this one stone shall be seven eyes; Behold, I will engrave the graving thereof, saith Jehovah of hosts; And I will remove the iniquity of this land in one day.
10 “‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
In that day, saith Jehovah of hosts, Shall ye invite every one his neighbor Under the vine and under the fig-tree.

< Zakariya 3 >