< Zakariya 3 >

1 Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
And he shows me Joshua the high priest standing before the Messenger of YHWH, and Satan standing at his right hand, to be an adversary to him.
2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
And YHWH says to Satan: “YHWH pushes against you, O Satan, Indeed, YHWH pushes against you, Who is fixing on Jerusalem, Is this not a brand delivered from fire?”
3 Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
And Joshua was clothed with filthy garments, and is standing before the Messenger.
4 Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
And He answers and speaks to those standing before Him, saying, “Turn aside the filthy garments from off him.” And He says to him, “See, I have caused your iniquity to pass away from off you, so as to clothe you with costly apparel.”
5 Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
He also said, “Let them set a pure turban on his head.” And they set the pure turban on his head, and clothe him with garments. And the Messenger of YHWH is standing,
6 Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
and the Messenger of YHWH protests to Joshua, saying,
7 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
“Thus said YHWH of Hosts: If you walk in My ways, And if you keep My charge, Then also you judge My house, And also you keep My courts, And I have given to you conductors among these standing by.
8 “‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
Now hear, O Joshua the high priest, You and your companions sitting before you (For men of type [are] they), For behold, I am bringing in My servant—a Shoot.
9 Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
For behold, the stone that I put before Joshua, On one stone [are] seven eyes, Behold, I am engraving its engraving, A declaration of YHWH of Hosts, And I have removed the iniquity of that land in one day.
10 “‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
In that day—a declaration of YHWH of Hosts, You call, each to his neighbor, To the place of the vine, And to the place of the fig tree!”

< Zakariya 3 >