< Zakariya 2 >

1 Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
Levantei os olhos, e vi, e eis que um homem com uma linha de medição na mão.
2 Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
Então perguntei: “Para onde você vai?”. Ele me disse: “Para medir Jerusalém, para ver qual é sua largura e qual é seu comprimento”.
3 Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
Eis que o anjo que falou comigo saiu, e outro anjo saiu ao seu encontro,
4 ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
e lhe disse: “Corra, fale com este jovem, dizendo: 'Jerusalém será habitada como aldeias sem muros, por causa da multidão de homens e gado que há nela.
5 Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
Pois eu”, diz Javé, “serei para ela um muro de fogo ao seu redor, e eu serei a glória no meio dela”.
6 “Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
Venha! Venha! Fuja da terra do norte', diz Yahweh; 'pois eu os espalhei no exterior como os quatro ventos do céu', diz Yahweh.
7 “Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
'Venha, Zion! Fuja, você que mora com a filha da Babilônia'.
8 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
Pois Javé de Exércitos diz: 'Por honra ele me enviou às nações que te saquearam; pois aquele que te toca toca na maçã de seu olho'.
9 Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
Pois eis que eu apertarei minha mão sobre eles, e eles serão um saque para aqueles que os serviram; e sabereis que Javé dos Exércitos me enviou”.
10 “Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
Sing e regozije-se, filha de Sião! Pois eis que eu venho e habitarei dentro de ti”, diz Javé.
11 “Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
Many nações se unirão a Javé nesse dia, e serão meu povo; e habitarei entre vós, e sabereis que Javé dos Exércitos me enviou a vós.
12 Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
Iavé herdará Judá como sua porção na terra santa, e escolherá novamente Jerusalém.
13 Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”
Silêncio, toda carne, perante Javé; pois ele se despertou de sua santa morada”!

< Zakariya 2 >