< Zakariya 2 >

1 Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
J'élevai encore mes yeux, et regardai; et voilà un homme qui avait à la main un cordeau à mesurer,
2 Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
Auquel je dis: Où vas-tu? Et il me répondit: Je vais mesurer Jérusalem, pour voir quelle est sa largeur, et quelle est sa longueur.
3 Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
Et voici, l'Ange qui parlait avec moi sortit, et un autre Ange sortit au-devant de lui;
4 ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
Et lui dit: Cours, et parle à ce jeune homme-là, en disant: Jérusalem sera habitée sans murailles, à cause de la multitude d'hommes et de bêtes qui seront au milieu d'elle.
5 Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
Mais je lui serai, dit l'Eternel, une muraille de feu tout autour, et je serai pour gloire au milieu d'elle.
6 “Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
Ha! Fuyez, fuyez hors du pays de l'Aquilon, dit l'Eternel: car je vous ai dispersés vers les quatre vents des cieux, dit l'Eternel.
7 “Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
Ha! Sion qui demeures avec la fille de Babylone, sauve-toi.
8 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
Car ainsi a dit l'Eternel des armées, lequel après la gloire m'a envoyé vers les nations qui vous ont pillés, que qui vous touche, touche la prunelle de son œil.
9 Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
Car voici, je vais lever ma main sur eux, et ils seront en proie à leurs serviteurs, et vous connaîtrez que l'Eternel des armées m'a envoyé.
10 “Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
Réjouis-toi avec chant de triomphe, et t'égaye, fille de Sion; car voici, je viens, et j'habiterai au milieu de toi, dit l'Eternel.
11 “Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
Et plusieurs nations se joindront à l’Eternel en ce jour-là, et deviendront mon peuple; et j'habiterai au milieu de toi; et tu sauras que l'Eternel des armées m'a envoyé vers toi.
12 Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
Et l'Eternel héritera Juda pour son partage en la terre de sa sainteté, et il choisira encore Jérusalem.
13 Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”
Que toute chair se taise, devant la face de l'Eternel, car il s'est réveillé de la demeure de sa sainteté.

< Zakariya 2 >