< Zakariya 2 >
1 Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
And I lifted up my eyes, and looked, and behold, there was a man with a measure-cord in his hand.
2 Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
Then said I, Whither art thou going? And he said unto me, To measure Jerusalem, to see what is her breadth, and what is her length.
3 Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
And, behold, the angel that spoke with me went out, and another angel came out to meet him;
4 ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
And he said unto him, Run, speak to this young man, saying, Without walls shall Jerusalem be inhabited because of the multitude of men and cattle in her midst.
5 Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
But I—I will be unto her, saith the Lord, a wall of fire round about, and for glory will I be in the midst of her.
6 “Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
Up! up! and flee away from the land of the north saith the Lord; for as the four winds of the heaven have I spread you abroad, saith the Lord.
7 “Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
Up, Zion, escape, thou that dwellest with the daughter of Babylon.
8 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
For thus hath said the Lord of hosts, For the sake of [your] glory hath he sent me unto the nations that have despoiled you; for whoever toucheth you, toucheth the apple of his eye.
9 Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
For, behold, I will swing my hand over them, and they shall be a spoil to those that served them: and ye shall acknowledge that the Lord of hosts hath sent me.
10 “Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
Sing, and rejoice, O daughter of Zion; for, lo, I am coming, and I will dwell in the midst of thee, saith the Lord.
11 “Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
And many nations will join themselves to the Lord on that day, and they shall be unto me for a people: and I will dwell in the midst of thee, and thou shalt know that the Lord of hosts hath sent me unto thee.
12 Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
And the Lord will take Judah as his inheritance upon the holy land; and he will again make choice of Jerusalem.
13 Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”
Be silent, all flesh! before the Lord; for he is waked up out of his holy habitation.