< Zakariya 2 >
1 Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
And I lifted up my eyes, and I saw, and behold, a man, and in his hand was a measuring line.
2 Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
And I said, “Where are you going?” And he said to me, “To measure Jerusalem, so that I may see how great its width and how great its length may be.”
3 Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
And behold, the angel, who had been speaking with me, departed, and another angel went out to meet him.
4 ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
And he said to him: Hurry, speak to this young man, saying: Jerusalem will be inhabited without walls, because of the multitude of men and beasts of burden in its midst.
5 Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
And I will be to it, says the Lord, a wall of fire all around. And in glory, I will be in its midst.
6 “Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
O, O flee from the land of the North, says the Lord, for I have scattered you into the four winds of heaven, says the Lord.
7 “Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
O Zion, flee, you who dwell with the daughter of Babylon.
8 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
For thus says the Lord of hosts: After the glory, he has sent me to the Gentiles, which have despoiled you. For he who touches you, touches the pupil of my eye.
9 Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
For behold, I lift up my hand over them, and they will be a prey to those who had served them. And you will know that the Lord of hosts has sent me.
10 “Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
Sing praise and rejoice, daughter of Zion. For behold, I approach, and I will dwell in your midst, says the Lord.
11 “Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
And many nations will be joined to the Lord in that day, and they will be my people, and I will dwell in your midst. And you will know that the Lord of hosts has sent me to you.
12 Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
And the Lord will possess his portion, Judah, in the sanctified land, and still he will single out Jerusalem.
13 Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”
Let all flesh be silent before the face of the Lord: for he has arisen from his holy dwelling place.