< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
İşte RAB'bin günü geliyor! Ey Yeruşalim halkı, senden yağmalanan mal gözlerinin önünde paylaşılacak.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
Yeruşalim'e karşı savaşmaları için bütün ulusları bir araya getireceğim. Kent ele geçirilecek, evler yağmalanacak, kadınların ırzına geçilecek. Kentte yaşayanların yarısı sürgüne gönderilecek, geri kalanlar kentte kalacak.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Sonra RAB, savaş zamanlarında yaptığı gibi, gidip bu uluslara karşı savaşacak.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
O gün O'nun ayakları Yeruşalim'in doğusundaki Zeytin Dağı'nın üzerinde duracak. Zeytin Dağı doğuya ve batıya doğru ortadan yarılıp çok büyük bir vadi oluşturacak. Dağın yarısı kuzeye, öbür yarısı güneye çekilecek.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
Yarılan dağımın oluşturduğu vadiden kaçacaksınız, çünkü vadi Asal'a dek uzanacak. Yahuda Kralı Uzziya döneminde depremden nasıl kaçtıysanız, öyle kaçacaksınız. O zaman Tanrım RAB bütün kutsallarla birlikte gelecek!
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
O gün ışık olmayacak, ışık veren cisimler kararacak.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Özel bir gün, yalnız RAB'bin bildiği bir gün olacak. Gece de gündüz de olmayacak. Gece aydınlık olacak.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
O gün Yeruşalim'in içinden diri sular akacak. Yaz kış suların yarısı Lut Gölü'ne, öbür yarısı Akdeniz'e akacak.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
RAB bütün dünyanın kralı olacak. O gün yalnız RAB, yalnız O'nun adı kalacak.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
Bütün ülke Geva'dan Yeruşalim'in güneyindeki Rimmon'a dek Arava Ovası gibi olacak. Ama Yeruşalim yükseltilecek ve Benyamin Kapısı'ndan ilk kapıya, Köşe Kapısı'na, Hananel Kulesi'nden kralın üzüm sıkma çukurlarına dek yerli yerinde duracak.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
İnsanlar oraya yerleşip güvenlik içinde yaşayacak. Yeruşalim bir daha yıkıma uğramayacak.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
Yeruşalim'e karşı savaşan bütün halkları RAB şu belayla cezalandıracak: Daha sağken bedenleri, gözleri, dilleri çürüyecek.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
O gün RAB insanları büyük dehşete düşürecek. Herkes yanındakinin elini yakalayacak, birbirlerine saldıracaklar.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
Yahudalılar da Yeruşalim'de savaşacak. Çevredeki bütün ulusların serveti, çok miktarda altın, gümüş, giysi toplanacak.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
Düşman ordugahlarındaki bütün hayvanlar da –at, katır, deve, eşek– benzer bir belaya çarptırılacak.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Yeruşalim'e saldıran uluslardan sağ kalanların hepsi Her Şeye Egemen RAB olan Kral'a tapınmak ve Çardak Bayramı'nı kutlamak için yıldan yıla Yeruşalim'e gidecekler.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
Yeryüzü halklarından hangisi Her Şeye Egemen RAB olan Kral'a tapınmak için Yeruşalim'e gitmezse, ülkesine yağmur yağmayacak.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Mısırlılar bunlara katılıp Yeruşalim'e gitmezlerse, RAB onları da Çardak Bayramı'nı kutlamak için Yeruşalim'e gitmeyen bütün ulusların başına getirdiği aynı belayla cezalandıracak.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Mısırlılar'a ve Çardak Bayramı'nı kutlamak için Yeruşalim'e gitmeyen bütün uluslara verilecek ceza budur.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
O gün atların çıngırakları üzerine, “RAB'be adanmıştır” diye yazılacak. RAB'bin Tapınağı'ndaki kazanlar da sunağın önündeki çanaklar gibi olacak.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
Yeruşalim ve Yahuda'da her kazan Her Şeye Egemen RAB'be adanacak. Kurban kesmeye gelenler bu kazanları kurban etini pişirmek için kullanacaklar. O gün Her Şeye Egemen RAB'bin Tapınağı'nda artık tüccar bulunmayacak.

< Zakariya 14 >