< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Eis que o dia do Senhor vem; repartir-se-hão no meio de ti os teus despojos.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
Porque eu ajuntarei todas as nações para a peleja contra Jerusalem; e a cidade será tomada, e as casas serão saqueadas, e as mulheres forçadas; e metade da cidade sairá para o captiveiro, mas o resto do povo não será extirpado da cidade.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
E o Senhor sairá, e pelejará contra estas nações, como no dia em que pelejou no dia da batalha.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
E n'aquelle dia estarão os seus pés sobre o monte das Oliveiras, que está defronte de Jerusalem para o oriente; e o monte das Oliveiras será fendido pelo meio, para o oriente e para o occidente, n'um valle muito grande; e metade do monte se apartará para o norte, e a outra metade d'elle para o sul.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
E fugireis ao valle dos meus montes (porque o valle dos montes chegará até Asel), e fugireis assim como fugistes de diante do terremoto nos dias de Uzias, rei de Judah: então virá o Senhor meu Deus, e todos os sanctos comtigo, ó Senhor.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
E será que n'aquelle dia não haverá preciosa luz nem espessa escuridão.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Mas será um dia o qual é conhecido do Senhor; nem dia nem noite será: e acontecerá que no tempo da tarde haverá luz.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
N'aquelle dia tambem acontecerá que sairão de Jerusalem aguas vivas, metade d'ellas para o mar oriental, e metade d'ellas até ao mar occidental: no estio e no inverno succederá isto.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
E o Senhor será rei sobre toda a terra: n'aquelle dia um só será o Senhor, e um só será o seu nome
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
Toda a terra ao redor se tornará em planicie, desde Geba até Rimmon, da banda do sul de Jerusalem, e será exalçada, e habitada no seu logar, desde a porta de Benjamin até ao logar da primeira porta, até á porta da esquina, e desde a torre de Hananeel até aos logares do rei.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
E habitarão n'ella, e não haverá mais anathema, porque Jerusalem habitará segura.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
E esta será a praga com que o Senhor ferirá a todos os povos que guerrearam contra Jerusalem: fará consumir a carne, estando elles em pé, e lhes apodrecerão os olhos nas suas covas, e lhes apodrecerá a lingua de cada um na sua bocca
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
N'aquelle dia tambem acontecerá que haverá uma grande perturbação do Senhor entre elles; porque pegará cada um na mão do seu companheiro, e alçar-se-ha a mão de cada um contra a mão do seu companheiro.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
E tambem Judah pelejará contra Jerusalem, e se ajuntarão em redor as riquezas de todas as nações, oiro e prata e vestidos em grande abundancia.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
Assim tambem será a praga dos cavallos, dos mulos, dos camelos e dos jumentos, e de todos os animaes que estiverem n'aquelles exercitos, como foi a praga d'elles.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
E será que, todos os que restarem de todas as nações que vieram contra Jerusalem, subirão de anno em anno para adorarem o Rei, o Senhor dos Exercitos, e celebrarem a festa das cabanas.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
E acontecerá que, se alguma das familias da terra não subir a Jerusalem, para adorar o Rei, o Senhor dos Exercitos, não virá sobre elles a chuva.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
E, se a familia dos egypcios, sobre os quaes não vem a chuva, não subir, nem vier, virá sobre elles a praga com que o Senhor ferirá as nações que não subirem a celebrar a festa das cabanas.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Este será o peccado dos egypcios e o peccado de todas as nações que não subirem a celebrar a festa das cabanas.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
N'aquelle dia será inscripto sobre as campainhas dos cavallos: sanctidade ao Senhor; e as panellas na casa do Senhor serão como as bacias diante do altar.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
E todas as panellas em Jerusalem e Judah serão sanctas ao Senhor dos Exercitos, e todos os que sacrificarem virão, e d'ellas tomarão, e n'ellas cozerão: e não haverá mais cananita na casa do Senhor dos Exercitos n'aquelle dia.

< Zakariya 14 >