< Zakariya 14 >
1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Se, det kommer en Herrens dag, da det hærfang som er tatt fra dig, skal skiftes ut i din midte;
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
for jeg vil samle alle hedningefolkene til krig mot Jerusalem, og staden skal bli tatt og husene bli plyndret, og kvinnene bli skjendet, og halvdelen av staden skal måtte gå i landflyktighet, men resten av folket skal ikke utryddes av staden.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
For Herren skal dra ut og stride mot disse hedningefolk, som han før har stridt på kampens dag.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
På den dag skal hans føtter stå på Oljeberget, som ligger midt imot Jerusalem i øst, og Oljeberget skal revne tvert over mot øst og vest, så der blir en stor dal, idet den ene halvdel av fjellet viker mot nord, og den andre halvdel mot syd.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
Og I skal fly til dalen mellem mine fjell, for dalen mellem fjellene skal nå like til Asel; I skal fly som I flydde for jordskjelvet i Judas konge Ussias' dager. Da skal Herren min Gud komme, og alle hellige med dig, min Gud.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
På den dag skal lyset bli borte; de herlige himmellys skal formørkes.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Og det skal komme én dag - Herren kjenner den - det skal hverken være dag eller natt; men mot aftens tid, da skal det bli lys.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
Og på den dag skal levende vann strømme ut fra Jerusalem, den ene halvdel av dem til havet i øst og den andre halvdel av dem til havet i vest; både sommer og vinter skal det være så.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
Da skal Herren bli konge over hele landet; på den dag skal Herren være én, og hans navn ett.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
Og hele landet, fra Geba til Rimmon sønnenfor Jerusalem, skal bli som den øde mark, og det skal heve sig høit og trone på sitt sted, like fra Benjamin-porten til det sted hvor den forrige port var, til Hjørneporten, og fra Hananels tårn til kongens vinperser.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
Og folket skal bo der, og der skal aldri mere lyses bann over det; Jerusalem skal ligge der trygt.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
Men denne plage skal Herren la ramme alle de folk som har stridt imot Jerusalem: Han skal la kjøttet råtne på dem alle mens de står på sine føtter, og deres øine skal råtne i sine huler, og tungen skal råtne i deres munn.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
På den dag skal Herren sende en stor redsel over dem, så de tar fatt på hverandre og løfter hånd mot hverandre.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
Også Juda skal stride i Jerusalem, og fra alle kanter skal hedningefolkenes gods sankes sammen, gull og sølv og klær i stor mengde.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
Den samme plage skal også ramme hestene, muleslene, kamelene, asenene og alle de andre dyr i leirene.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Og alle de som blir igjen av alle de hedningefolk som angrep Jerusalem, skal år efter år dra op for å tilbede Kongen, Herren, hærskarenes Gud, og for å delta i løvsalenes fest.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
Men om noget av jordens folk ikke drar op til Jerusalem for å tilbede Kongen, Herren, hærskarenes Gud, så skal det ikke komme regn hos dem;
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
om Egyptens folk ikke drar op og ikke møter frem, da skal det ikke komme regn hos dem heller; den samme plage skal ramme dem som Herren lar ramme de hedningefolk som ikke drar op for å delta i løvsalenes fest.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Sådan skal den straff være som rammer Egypten og alle de hedningefolk som ikke drar op for å delta i løvsalenes fest.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
På den dag skal det stå på hestenes bjeller: Helliget til Herren, og grytene i Herrens hus skal være som offerskålene foran alteret,
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
og hver gryte i Jerusalem og i Juda skal være helliget til Herren, hærskarenes Gud, og alle de som ofrer, skal komme og ta av dem til å koke i; og det skal ikke mere være nogen kana'anitt i Herrens, hærskarenes Guds hus på den dag.