< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
A IA HOI, e hele mai ana ka la o Iehova, e puunaueia'i kou waiwai pio mawaena ou.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
E houluulu auanei au i na lahuikanaka a pau e ku e ia Ierusalema i ke kaua; A e hoopioia auanei ke kulanakauhale, E haoia na hale, a e moe wale ia na wahine: A e hele pio aku kekahi hapalua o ko ke kulanakauhale, Aka, aole e hookiia'e ke koena o kanaka mai ke kulanakauhale aku.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Alaila hoi, e hele aku ai o Iehova, A e kaua aku i kela mau lahuikanaka, E like me kana i kaua aku ai i ka la hoouka kaua.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
A e ku kona mau wawae ia la maluna o ka mauna Oliveta, E ku ana i ke alo o Ierusalema ma ka hikina; A e naha iho ka mauna Oliveta, mawaenakonu ona, Mai ka hikina a ke komohana, he awawa nui loa; A e nee aku kekahi hapalua o ka mauna ma ke kukulu akau, A o kekahi ma ke kukulu hema.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
A e holo aku oukou i ke awawa o na mauna o'u, No ka mea, e hiki aku ana ke awawa o na mauna i Azala; A e holo oukou e like me ko oukou holo ana i ke olai, I na la o Uzia, o ke alii o ka Iuda: A e hele mai ana o Iehova o ko'u Akua, a me na haipule a pau me ia.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
Eia hoi kekahi ia la, Aole no he malamalama, nalowale na hoku nani.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Hookahi no ia la, E ikea auanei ia e Iehova, aohe ao, aohe po; A i ka wa ahiahi e malamalama auanei ia.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
E hiki no ia la, e kahe aku ka wai ola mai Ierusalema aku, O kekahi hapa ma ke kai hikina, A o kela hapa ma ke kai komohana; A pela no ia i ke kau a me ka hooilo.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
A e lilo auanei o Iehova i Alii maluna o ka honua a pau: Ia la hoi e hookahi auanei o Iehova, e hookahi hoi kona inoa.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
E hoololiia ka aina a pau a like me ka papu Mai o Geba aku a hiki i Rimona ma ke kukuluhema o Ierusalema: E hookiekieia'e ia, a e hoonoho paa ia ma kona wahi, Mai ka ipuka o Beniamina a hiki i kahi o ka puka mua, A i ka puka kihi; A mai ka halekiai o Hananela a hiki i na luawaina o ke alii.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
A e noho lakou iloko ona, aole hoi e luku hou ia oia, Aka, e nohoia o Ierusalema me ka maluhia.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
Eia hoi ka mai a Iehova e hahau mai ai, I na kanaka a pau i kaua aku ai ia Ierusalema; E hoowiwi auanei oia i ko lakou kino, Ia lakou e ku ana maluna o ko lakou wawae, A e emi iho ko lakou mau maka maloko o ko lakou mau lua, A e pau iho ko lakou alelo maloko o ko lakou waha.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
E hiki hoi ia la he haunaele nui no Iehova mai, iwaena o lakou; A e lalau aku kekahi i ka lima o kona hoa, A e ku e kona lima iluna i ka lima o kona hoa.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
A e kaua aku hoi ka Iuda ia Ierusalema; Aka, e houluuluia ka waiwai o ko na aina e a puni, O ke gula, ke kala, a me na lole aahu he nui loa.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
A pela hoi ka mai ana o na lio, na hoki, o na kamelo, o na miula, a o na holoholona a pau, Iloko o kahi a lakou e hoomoana ai, e like me kela mai.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Eia hoi keia, o na mea a pau e koe, O na lahuikanaka a pau i hele ku e mai ia Ierusalema, E pii ae lakou i kela makahiki i keia makahiki, E hoomana i ke Alii ia Iehova o na kaua, A e malama i ka ahaaina kauhalelewa.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
A o ka mea pii ole i Ierusalema, O na lahuikanaka o ka honua e hoomana i ke Alii ia Iehova o na kaua, Maluna ona e haule ole ai ka ua.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Ina paha hoi e pii ole mai, Aole hoi e hele mai ko Aigupita, kahi e ole ai ka ua, Ilaila no e loohia'i ka mai a Iehova e kau mai ai maluna o na lahuikanaka, I pii ole e malama i ka ahaaina kauhalelewa.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Oia ka hoohewaia o ko Aigupita, A me ka hoohewaia o na lahuikanaka a pau, I pii ole aku e malama i ka ahaaina kauhalelewa.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
Ia la no, e kakauia'i maluna o na kahiko ana o na lio, UA LAA NO IEHOVA: A e like auanei na ipu iloko o ka hale o Iehova me na kiaha imua o ke kuahu.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
A e lilo na ipu a pau iloko o Ierusalema a iloko o ka Iuda, I laa no Iehova o na kaua; A e hele mai ka poe mohai a pau, A e lawe i keia mau mea, a e hoolapalapa iloko: Ia la hoi, aole e komo hou aku ko Kanaana, Iloko o ka hale o Iehova o na kaua.

< Zakariya 14 >