< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Voici, il vient un jour pour l'Eternel, et tes dépouilles seront partagées au milieu de toi, [Jérusalem].
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
J'assemblerai donc toutes les nations en bataille contre Jérusalem, et la ville sera prise, et les maisons pillées, et les femmes violées, et la moitié de la ville sortira en captivité, mais le reste du peuple ne sera point retranché de la ville.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Car l'Eternel sortira, et combattra contre ces nations-là, comme il a combattu au jour de la bataille.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
Et ses pieds se tiendront debout en ce jour-là sur la montagne des Oliviers, qui est vis-à-vis de Jérusalem, du côté d'orient; et la montagne des Oliviers sera fendue par le milieu, vers l'Orient et l'Occident, de sorte qu'il y aura une très-grande vallée; et une moitié de la montagne se retirera vers l'Aquilon, et l'autre moitié vers le Midi.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
Et vous fuirez par cette vallée de montagnes; car il fera joindre cette vallée de montagnes jusqu'à Atsal; et vous fuirez comme vous vous enfuites de devant le tremblement de terre, aux jours d'Hozias Roi de Juda; alors l'Eternel mon Dieu viendra, et tous les saints seront avec toi.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
Et il arrivera qu'en ce jour-là, la lumière précieuse ne sera pas mêlée de ténèbres.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Mais le jour sera sans mélange, lequel sera connu de l'Eternel: Il n'y aura point une alternative de jour et de nuit, mais au temps du soir il y aura de la lumière.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
Et il arrivera qu'en ce jour-là des eaux vives sortiront de Jérusalem; la moitié d'elles ira vers la mer d'Orient; et l'autre moitié, vers la mer d'Occident; il y en aura en été et en hiver.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
Et l'Eternel sera Roi sur toute la terre; en ce jour-là il n'y aura qu'un seul Eternel, et son nom ne sera qu'un.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
Et toute la terre deviendra comme la campagne depuis Guébah jusqu'à Rimmon, vers le Midi de Jérusalem, laquelle sera exaltée et habitée en sa place, depuis la porte de Benjamin, jusqu'à l'endroit de la première porte, et jusqu'à la porte des encoignures, et depuis la tour de Hananéel, jusqu'aux pressoirs du Roi.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
On y demeurera, et il n'y aura plus d'interdit, mais Jérusalem sera habitée en sûreté.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
Or ce sera ici la plaie de laquelle l'Eternel frappera tous les peuples qui auront fait la guerre contre Jérusalem; il fera que la chair de chacun se fondra, eux étant sur leurs pieds; et leurs yeux se fondront dans leurs orbites, et leurs langues se fondront dans leur bouche.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
Et il arrivera en ce jour-là qu'il y aura un grand trouble entre eux par l'Eternel; car chacun saisira la main de son prochain, et la main de l'un s'élèvera contre la main de l'autre.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
Juda aussi combattra à Jérusalem, et les richesses de toutes les nations d'alentour y seront assemblées: l'or, et l'argent, et des vêtements en très grand nombre.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
Aussi la plaie des chevaux, des mulets, des chameaux et des ânes, et de toutes les bêtes qui seront en ces champs-là, sera telle que la plaie précédente.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Et il arrivera que tous ceux qui seront restés de toutes les nations venues contre Jérusalem, monteront en foule chaque année pour se prosterner devant le Roi, l'Eternel des armées, et pour célébrer la fête des Tabernacles.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
Et il arrivera que quiconque d'entre les familles de la terre ne sera point monté à Jérusalem, pour se prosterner devant le Roi, l'Eternel des armées, il n'y aura point de pluie sur eux.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Et si la famille d'Egypte n'y monte point, et qu'elle n'y vienne point, quoiqu'il n'y ait point [de pluie] sur eux, ils seront [frappés] de cette plaie dont l'Eternel frappera les nations qui ne seront point montées pour célébrer la fête des Tabernacles.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Tel sera le péché d'Egypte, et le péché de toutes les nations qui ne seront point montées pour célébrer la fête des Tabernacles.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
En ce temps-là il sera [écrit] sur les sonnettes des chevaux: LA SAINTETÉ A L'ETERNEL; et il y aura des chaudières dans la maison de l'Eternel, autant que de bassins devant l'autel.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
Et toute chaudière qui sera dans Jérusalem et en Juda, sera sainteté à l'Eternel des armées; et tous ceux qui sacrifieront, viendront, et en prendront, et y cuiront; et il n'y aura plus en ce jour-là de Cananéen dans la maison de l'Eternel des armées.

< Zakariya 14 >