< Zakariya 14 >
1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Voici que les jours du Seigneur arrivent; et tes dépouilles au milieu de toi vont être partagées.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
Et Je rassemblerai toutes les nations pour qu'elles combattent contre Jérusalem; et la ville sera prise, et les maisons seront livrées au pillage, et les femmes seront profanées; et la moitié des habitants sera emmenée captive, et le reste de Mon peuple ne sera point massacré dans la ville.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Et le Seigneur sortira et Il combattra les gentils, comme Il combat au jour de la bataille.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
Et ce jour-là Ses pieds poseront sur la montagne des Oliviers, vis-à-vis de Jérusalem, du côté de l'Orient. Et la montagne des Oliviers se fendra, moitié vers l'Orient, moitié du côté de la mer; il y aura entre les deux moitiés un immense ravin. Et l'une des deux moitiés s'inclinera au nord, et l'autre au midi.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
Et la gorge de Mes montagnes se fermera; et la gorge des montagnes sera resserrée jusqu'à Jasod, et elle sera close comme elle l'a été du temps du tremblement de terre, durant les jours d'Ozias, roi de Juda. Et le Seigneur mon Dieu viendra, et tous Ses saints avec Lui.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
Et voici ce qui arrivera: en ce jour-là il n'y aura point de lumière, mais du froid et de la gelée qui
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
dureront tout le jour; et ce jour-là sera connu du Seigneur, et ce ne sera pas le jour, et ce ne sera pas la nuit; et, sur le soir, il y aura une lumière.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
Et ce jour-là une eau vive sortira de Jérusalem, et la moitié coulera à la première mer, et l'autre moitié à la dernière; et il en sera ainsi pendant le printemps et l'été.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
Et le Seigneur sera roi de toute la terre; et ce jour-là le Seigneur sera le seul Dieu, et Son Nom sera un,
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
tout autour de la terre et du désert de Gaza à Remmon, au midi de Jérusalem. Rama subsistera où il est, de la porte de Benjamin à la place de l'ancienne porte, et à la porte des Angles, et de la tour d'Anaméel aussi loin que les pressoirs du roi.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
Jérusalem sera repeuplée; elle ne sera plus frappée d'anathème, et elle sera assise en assurance.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
Et voici le fléau dont le Seigneur frappera tous les peuples qui auront marché contre elle. Leurs chairs se liquéfieront, eux debout sur leurs pieds; leurs yeux s'écouleront hors de leurs orbites, et leur langue se liquéfiera dans leur bouche.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
Et ce jour-là voici ce qui arrivera: il y aura contre eux un grand transport du Seigneur; et ils se prendront par la main les uns les autres, et les mains entrelaceront les mains.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
Et Juda se rangera en bataille contre Jérusalem; et on recueillera les richesses de tous les peuples d'alentour, l'or, l'argent et des vêtements innombrables.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
Et les chevaux, les mulets, les chameaux, les ânes et toutes les bêtes qui seront dans les camps seront pareillement détruits.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Voici ce qui arrivera: les survivants parmi les gentils qui auront marché contre Jérusalem y monteront chaque année pour y adorer le Roi, Seigneur tout-puissant, et pour célébrer la fête des Tabernacles.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
Et voici ce qui arrivera: si de toutes les tribus de la terre on ne monte pas à Jérusalem pour adorer le Roi, Seigneur tout-puissant, ceux qui s'en abstiendront seront pareillement punis.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Et s'il est une des tribus de l'Égypte qui ne monte pas au temple, les mêmes fléaux l'atteindront; elle sera frappée comme toutes les nations qui ne viendront pas célébrer la fête des Tabernacles.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Ce sera le péché de l'Égypte, et le péché de toutes mes nations qui ne viendront pas célébrer la fête des tabernacles.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
Et ce jour-là tout ce qui orne le frein des chevaux sera consacré au Seigneur tout-puissant; les chaudières seront dans le temple du Seigneur comme les coupes devant l'autel.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
Et toutes les chaudières de Jérusalem et de Juda seront consacrées au Seigneur tout-puissant. Et tous ceux qui offriront des sacrifices viendront, et ils prendront de ces chaudières, et ils s'en serviront pour faire cuire les victimes; et ce jour-là il n'y aura plus de Chananéens dans la maison du Seigneur tout-puissant.