< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
There! a day [is] coming of Yahweh and it will be divided plunder your in midst your.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
And I will gather all the nations - to Jerusalem for battle and it will be captured the city and they will be plundered the houses and the women (they will be lain with *Q(K)*) and it will go out half of the city in exile and [the] rest of the people not it will be cut off from the city.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
And he will go forth Yahweh and he will fight against the nations those like [the] day (fought he *L(abh)*) in a day of battle.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
And they will stand feet his on the day that on [the] mountain of Olives which [is] on [the] face of Jerusalem from [the] east and it will be split open [the] mountain of Olives from middle its east-ward and west-ward a valley great very and it will depart half of the mountain north-ward and half of it south-ward.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
And you will flee [the] valley of mountains my for it will reach [the] valley of mountains to Azal and you will flee just as you fled from before the earthquake in [the] days of Uzziah [the] king of Judah and he will come Yahweh God my all holy [ones] [will be] with you.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
And it will be on the day that not it will be light splendid [ones] (and frost. *Q(K)*)
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
And it will be a day one it it will be known to Yahweh not day and not night and it will be to [the] time of evening it will be light.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
And it will be - on the day that they will go out waters living from Jerusalem half of them to the sea eastern and half of them to the sea western in the summer and in the winter it will be.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
And he will become Yahweh king over all the earth on the day that he will be Yahweh one and name his one.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
It will change all the land like the Arabah from Geba to Rimmon [the] south of Jerusalem and it will rise and it will remain in place its from [the] gate of Benjamin to [the] place of [the] gate first to [the] gate of the corners and [the] tower of Hananel to [the] wine-presses of the king.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
And people will dwell in it and total destruction not it will be again and it will remain Jerusalem to security.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
And this - it will be the plague which he will strike Yahweh all the peoples which they have waged war on Jerusalem he will cause to rot - flesh its and it [is] standing on feet its and eyes its they will rot in sockets their and tongue its it will rot in mouth their.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
And it will be on the day that it will be a panic of Yahweh great among them and they will take hold of each [the] hand of neighbor his and it will go up hand his on [the] hand of neighbor his.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
And also Judah it will fight at Jerusalem and it will be gathered [the] wealth of all the nations all around gold and silver and garments to abundance very great.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
And thus it will be [the] plague of the horse the mule the camel and the donkey and all the livestock which it will be in the camps those like the plague this.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
And it will be every [one who] remains of all the nations which came on Jerusalem and they will go up as often as a year in a year to bow down to [the] king Yahweh of hosts and to celebrate a festival [the] festival of Tabernacles.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
And it will be [one] who not he will go up from with [the] clans of the earth to Jerusalem to bow down to [the] king Yahweh of hosts and not on them it will be rain.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
And if [the] clan of Egypt not it will go up and not [is] going and not on them it will be the plague which he will strike Yahweh the nations which not they will go up to celebrate a festival [the] festival of Tabernacles.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
This it will be [the] punishment for sin of Egypt and [the] punishment for sin of all the nations which not they will go up to celebrate a festival [the] festival of Tabernacles.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
On the day that it will be on [the] bells of the horse[s] holiness to Yahweh and it will be the pots in [the] house of Yahweh [will be] like the bowls before the altar.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
And it will be every pot in Jerusalem and in Judah a holy thing to Yahweh of hosts and they will come all those [who] sacrifice and they will take some of them and they will boil in them and not [he] will be a Canaanite again in [the] house of Yahweh of hosts on the day that.

< Zakariya 14 >