< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Watch out! For the day of the Lord is coming when what has been plundered from you will be divided up right in front of you.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
I will bring together all the nations to attack Jerusalem. The city will be captured, the houses looted, and the women raped. Half the population will be taken into exile, but the rest of the people will not be removed from the city.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Then the Lord will go out to fight against the nations as he fights in times of war.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
On that day his feet will stand on the Mount of Olives which faces Jerusalem to the east. The Mount of Olives will split apart, with half moving north and half moving south, creating a wide valley from east to west.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
You will run away through this mountain valley for it will reach as far as Azal. You will run away like people did at the time of the earthquake during the reign of Uzzah, king of Judah. Then the Lord will come, accompanied by all his holy ones.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
On that day there will be no longer cold and frost.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
It will be one continuous day (only the Lord knows how this could happen). It won't be day or night, because in the evening it will still be light.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
On that day living waters will flow out of Jerusalem, half of it going east to the Dead Sea and half going west to the Mediterranean Sea, flowing in summer and winter alike.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
The Lord will be king over all the earth. On that day there will be one true Lord, and his name the only one.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
The whole land will be transformed into a plain, from Geba to Rimmon, south of Jerusalem. But Jerusalem will be raised up to where it was, and people will live there from the Benjamin Gate to where the old gate was, to the Corner Gate, and from the Tower of Hananel to the king's winepresses.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
It will be inhabited and never again condemned to destruction again—people will be able to live in safety in Jerusalem.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
This will be the plague that the Lord will use to strike all the nations that attacked Jerusalem. Their flesh shall rot while they are still standing on their feet; their eyes will rot in their sockets; their tongues will rot in their mouths.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
On that day the Lord will strike them with a terrible panic, and they will seize one another, and fight hand-to-hand.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
Even Judah will fight in Jerusalem. The wealth of the surrounding nations shall be collected: lots of gold, silver, and clothes.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
A similar plague will strike the horses, mules, camels, donkeys, and all other animals that may be in their camps.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
After this every one of the survivors from the nations that attacked Jerusalem will go there to worship the King, the Lord Almighty, and to celebrate the Festival of Shelters.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
If any of the peoples of the world refuse to go to Jerusalem to worship the King, the Lord Almighty, they will have no rain.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
If the Egyptian people refuse to go and attend, then the Lord will inflict on them the same plague as on the other nations who will not go celebrate the Festival of Shelters.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
This will be the punishment on Egypt and all the nations if they do not go to Jerusalem and celebrate.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
On that day the bells worn by horses will be engraved with the words “Holy to the Lord.” The household cooking pots used in the Lord's Temple will be as holy as the bowls used on the altar in the presence of the Lord.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
Every pot in Jerusalem and in Judah will be holy to the Lord Almighty, so that everyone who comes to sacrifice can take them and cook their sacrificial meat in them. On that day there will no longer be traders in the Lord's Temple.

< Zakariya 14 >