< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Behold, the days of the Lord will arrive, and your spoils will be divided in your midst.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
And I will gather all the Gentiles in battle against Jerusalem, and the city will be captured, and the houses will be ravaged, and the women will be violated. And the central part of the city will go forth into captivity, and the remainder of the people will not be taken away from the city.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Then the Lord will go forth, and he will fight against those Gentiles, just as when he fought in the day of conflict.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
And his feet will stand firm, in that day, upon the Mount of Olives, which is opposite Jerusalem towards the East. And the mount of Olives will be divided down its center part, towards the East and towards the West, with a very great rupture, and the center of the mountain will be separated towards the North, and its center towards the Meridian.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
And you will flee to the valley of those mountains, because the valley of the mountains will be joined all the way to the next. And you will flee, just as you fled from the face of the earthquake in the days of Uzziah king of Judah. And the Lord my God will arrive, and all the saints with him.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
And this shall be in that day: there will not be light, only cold and frost.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
And there will be one day, which is known to the Lord, not day and not night. And in the time of the evening, there will be light.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
And this shall be in that day: the living waters will go out from Jerusalem, half of them towards the East sea, and half of them towards the furthest sea. They will be in summer and in winter.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
And the Lord will be King over all the earth. In that day, there will be one Lord, and his name will be one.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
And all the land will return even to the desert, from the hill of Rimmon to the South of Jerusalem. And she will be exalted, and she will dwell in her own place, from the gate of Benjamin even to the place of the former gate, and even to the gate of the corners, and from the tower of Hananel even to the pressing room of the king.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
And they will dwell in it, and there will be no further anathema, but Jerusalem shall sit securely.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
And this will be the plague by which the Lord will strike all the Gentiles that have fought against Jerusalem. The flesh of each one will waste away while they are standing on their feet, and their eyes will be consumed in their sockets, and their tongue will be consumed in their mouth.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
In that day, there will be a great tumult from the Lord among them. And a man will take the hand of his neighbor, and his hand will be clasped upon the hand of his neighbor.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
And even Judah will fight against Jerusalem. And the riches of all the Gentiles will be gathered together around them: gold, and silver, and more than enough garments.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
And, like the ruin of the horse, and the mule, and the camel, and the donkey, and all the beasts of burden, which will have been in those encampments, so will be this ruination.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
And all those who will be the remnant of all the Gentiles that came against Jerusalem, will go up, from year to year, to adore the King, the Lord of hosts, and to celebrate the feast of tabernacles.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
And this shall be: whoever will not go up, from the families of the earth to Jerusalem, so as to adore the King, the Lord of hosts, there will be no showers upon them.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
But if even the family of Egypt will go not up, nor approach, neither will it be upon them, but there will be ruin, by which the Lord will strike all the Gentiles, who will not go up to celebrate the feast of tabernacles.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
This will be the sin of Egypt, and this will be the sin of all the Gentiles, who will not go up to celebrate the feast of tabernacles.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
In that day, that which is on the bridle of the horse will be holy to the Lord. And even the cooking pots in the house of the Lord will be like holy vessels before the altar.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
And every cooking pot in Jerusalem and Judah will be sanctified to the Lord of hosts. And all those who make sacrifices will come and take from them, and will cook with them. And the merchant will no longer be in the house of the Lord of hosts, in that day.

< Zakariya 14 >