< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Gle, dolazi dan Jahvin kada će se podijeliti plijen usred tebe.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
I sabrat ću sve narode u Jeruzalem u borbu. I zaposjest će grad, opljačkati kuće i silovati žene. Polovina će grada otići u izgnanstvo, ali Ostatak neće biti istrijebljen iz grada.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
Tada će Jahve izaći i boriti se protiv tih naroda kako on zna ratovati u dan ratni.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
Noge će mu, u dan onaj, stajati na Gori maslinskoj koja je nasuprot Jeruzalemu na istoku. I raskolit će se Gora maslinska po srijedi, između istoka i zapada, u golemu dolinu: jedna će se polovina pomaknuti na sjever, druga na jug.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
Dolina Gore moje bit će ispunjena od Goe pa do Jasola i bit će zakrčena kao što je bila zakrčena poslije potresa u dane Uzije, kralja judejskog. Tada će doći Jahve, Bog tvoj, i svi sveci s njim.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
U dan onaj neće više biti ni studeni ni leda.
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
Bit će to dan čudesan - znade ga Jahve - ni dan ni noć; i u vrijeme večeribit će svjetlo.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
U onaj dan žive će vode poteći iz Jeruzalema, pola k moru istočnom, pola kmoru zapadnom. Bit će tako ljeti i zimi.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
I Jahve će biti kralj nad svom zemljom.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
Sva će se zemlja pretvoriti u ravnicu, od Gebe do Rimona negepskog. A Jeruzalem će se uzvisiti na svom mjestu; i bit će nastanjen - od Vrata Benjaminovih do Prvih vrata, to jest do Vrata ugaonih, i od Kule Hananeelove do Kraljeva tijeska.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
Opet će se stanovati u njemu, i više neće biti prokletstva; Jeruzalem će živjeti u miru.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
A evo kojom će ranom Jahve udariti sve narode koji budu zavojštili na Jeruzalem: meso će im se raspadati dok budu na nogama; oči će im trunuti u dupljama, jezik gnjiti u ustima.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
U dan onaj nastat će među njima silan metež od Jahve: jedan će drugoga za ruku hvatati, i ruka će se jednoga dizati na drugoga.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
I Juda će se boriti u Jeruzalemu. Tu će se sakupiti bogatstva svih okolnih naroda: zlato, srebro, odjeća u velikoj množini.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
A slična će rana pasti na konje, mazge, deve i magarce, i na svu stoku koja se nađe u tome taboru.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
Tko preživi od svih naroda koji dođu na Jeruzalem, uzlazit će godimice da se pokloni pred Kraljem, Jahvom nad Vojskama, i da slave Blagdan sjenica.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
Ako koje pleme zemlje ne uzađe u Jeruzalem da se pokloni pred Kraljem, Jahvom nad Vojskama, neće biti kiše za njega.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Ako li pleme egipatsko ne uzađe i ne dođe, stići će ga isti udarac kojim će Jahve udariti narode koji ne bi uzašli svetkovati Blagdan sjenica.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
Takva će biti kazna Egiptu i svim narodima koji ne budu uzašli da svetkuju Blagdan sjenica.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
U onaj dan stajat će na konjskim praporcima 'Jahvi posvećen'; a u Domu Jahvinu bit će lonci kao žrtvene čaše pred žrtvenikom;
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
i svaki će lonac u Jeruzalemu i u Judeji biti posvećen Jahvi nad Vojskama - svi koji budu htjeli žrtvovati uzimat će ih i kuhati u njima. I u dan onaj neće više biti trgovaca u Domu Jahve nad Vojskama.

< Zakariya 14 >