< Zakariya 13 >

1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
«در آن زمان برای خاندان داوود و مردم اورشلیم چشمه‌ای جاری خواهد شد، چشمه‌ای که ایشان را از همهٔ گناهان و ناپاکی‌هایشان پاک خواهد ساخت.»
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: «در آن روز هرگونه بت‌پرستی را در سراسر سرزمین اسرائیل برمی‌اندازم، به طوری که اثری از آن باقی نماند و نام بتها فراموش شود. سرزمین را به کلی از وجود انبیای دروغین و روح پلید پاک می‌کنم،
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
و اگر کسی باز به دروغ نبوّت کند، به دست پدر و مادر خودش کشته خواهد شد! به او خواهند گفت:”تو باید کشته شوی، چون به نام خداوند کاذبانه نبوّت می‌کنی.“
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
«در آن روز انبیای دروغین از نبوّتهایشان خجالت خواهند کشید و دیگر برای فریب دادن مردم لباس انبیا را بر تن نخواهند کرد.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
هر یک از آنها خواهند گفت:”من نبی نیستم، من یک کشاورزم و شغلم از جوانی کشاورزی بوده است.“
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
و اگر کسی بپرسد:”پس این زخمها روی بدن تو چیست؟“جواب می‌دهد:”در نزاع با دوستان زخمی شده‌ام.“»
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: «ای شمشیر بر ضد شبان من، آن مردی که همدوش و همکار من است، برخیز! شبان را بزن تا گوسفندان پراکنده شوند. من قوم خود را خواهم زد
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
و دو سوم آنها از بین خواهند رفت.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
یک سوم باقیمانده را از میان آتش می‌گذرانم و آنها را پاک می‌کنم، درست مثل طلا و نقره که به‌وسیلۀ آتش، خالص می‌شوند. ایشان نام مرا خواهند خواند و من آنها را اجابت خواهم نمود. من خواهم گفت:”اینها قوم من هستند.“و ایشان خواهند گفت:”یهوه خدای ماست.“»

< Zakariya 13 >