< Zakariya 13 >

1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
En ce jour-là, il y aura une fontaine ouverte à la maison de David et aux habitants de Jérusalem, pour laver le pécheur et la femme qui est dans ses mois.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
Et il arrivera en ce jour-là, dit le Seigneur des armées, que je détruirai de la terre les noms des idoles, et qu’on n’en conservera plus la mémoire; et les faux prophètes et l’esprit immonde, je les enlèverai de là terre.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
Et il arrivera que si quelqu’un prophétise encore, son père et sa mère qui l’ont engendré, lui diront: Tu ne vivras pas, parce que tu as proféré le mensonge au nom du Seigneur; et son père et sa mère, les auteurs de ses jours, le perceront, parce qu’il aura prophétisé.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
Et il arrivera en ce jour-là que les prophètes seront confondus, chacun par sa propre vision, lorsqu’il prophétisera; et ils ne se couvriront pas d’un sac, afin de mentir;
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
Mais chacun d’eux dira: Je ne suis point prophète; je suis un homme laboureur; car Adam est mon modèle depuis ma jeunesse.
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
Et on lui dira: Que sont ces plaies au milieu de tes mains? Et il dira: J’ai été percé de ces plaies que j’ai reçues dans la maison de ceux qui m’aimaient.
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
Ô épée à deux tranchants, réveille-toi; viens contre mon pasteur, contre l’homme qui se tient attaché à moi, dit le Seigneur des armées; frappe le pasteur, et les brebis seront dispersées; et je tournerai ma main vers les petits.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Et il y aura dans toute la terre, dit le Seigneur, deux parties qui seront dispersées, et qui défaudront, et la troisième partie y sera laissée.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
Et je ferai passer la troisième partie par le feu, et je la chaufferai fortement, comme on chauffe l’argent, et je l’éprouverai comme on éprouve l’or. Elle invoquera mon nom, et moi je l’exaucerai. Je lui dirai: Tu es mon peuple; et elle, elle dira: Le Seigneur est mon Dieu.

< Zakariya 13 >