< Zakariya 13 >
1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
« En ce jour-là, une fontaine sera ouverte à la maison de David et aux habitants de Jérusalem, pour le péché et pour l'impureté.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
En ce jour-là, dit l'Éternel des armées, j'effacerai du pays les noms des idoles, et on ne se souviendra plus d'elles. Je ferai aussi disparaître du pays les prophètes et l'esprit d'impureté.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
Si quelqu'un prophétise encore, son père et sa mère qui l'a enfanté lui diront: « Tu dois mourir, car tu dis des mensonges au nom de l'Éternel »; et son père et sa mère qui l'a enfanté le poignarderont quand il prophétisera.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
En ce jour-là, chacun des prophètes aura honte de sa vision quand il prophétisera, il ne portera pas de manteau de poils pour tromper,
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
mais il dira: « Je ne suis pas prophète, je suis laboureur de la terre, car j'ai été fait esclave dès ma jeunesse ».
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
On lui dira: « Qu'est-ce que c'est que ces plaies entre tes bras? ». Il répondra: « Ce sont les blessures que j'ai reçues dans la maison de mes amis ».
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
« Réveille-toi, épée, contre mon berger! et contre l'homme qui m'est proche, dit Yahvé des Armées. « Frappez le berger, et les brebis seront dispersées; et je tournerai ma main contre les petits.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Il arrivera que dans tout le pays, dit Yahvé, « deux parties en elle seront coupées et mourront; mais le troisième sera laissée dedans.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
Je ferai passer le tiers dans le feu, et les affinera comme on affine l'argent, et les testera comme on teste l'or. Ils invoqueront mon nom, et je les entendrai. Je dirai: « C'est mon peuple ». et ils diront: 'Yahvé est mon Dieu'".