< Zakariya 13 >

1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
“On that day a spring will be opened for the house of David and the inhabitants of Jerusalem, for their sin and impurity.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
On that day—this is the declaration of Yahweh of hosts—I will cut off the names of the idols from the land and they will no longer be remembered. I will remove the prophets and the spirit of impurity from the land.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
If any man continues to prophesy, his father and mother who bore him will tell him, 'You will not live, for you speak lies in the name of Yahweh!' Then the father and mother who bore him will pierce him when he prophesies.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
On that day each prophet will be ashamed of his vision when he is about to prophesy. These prophets will no longer wear a hairy cloak, in order to deceive the people.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
For each will say, 'I am not a prophet! I am a man who works the soil, for the land became my work while I was still a young man!'
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
But someone will say to him, 'What are these wounds between your arms?' and he will answer, 'I was wounded with those in my friends' house.'”
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
“Sword! Rouse yourself against my shepherd, the man who stands close to me— this is the declaration of Yahweh of hosts. Strike the shepherd, and the flock will scatter! For I will turn my hand against the lowly ones.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Then it will come about that throughout all the land—this is Yahweh's declaration— that two-thirds of it will be cut off! Those people will perish; only one-third will remain there.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
I will bring that third through the fire and refine them as silver is refined; I will test them as gold is tested. They will call on my name, and I will answer them and say, 'This is my people!' and they will say, 'Yahweh is my God!'”

< Zakariya 13 >