< Zakariya 13 >

1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
At that time [it will be as though] [MET] there will be a fountain from which water flows continually to cleanse the descendants [MTY] of [King] David and [all] the [other] people in Jerusalem from the guilt of the sins that they have committed, [especially] from becoming unacceptable to me [by worshiping idols].
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
The Commander of the armies of angels says, “At that time, I will prevent [people from even mentioning] the names of the idols in their country, and no one will remember them any more. I will also expel from the land all the people who falsely claim that they are prophets [DOU].
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
If someone continues to prophesy [falsely], his parents must say to him, ‘You have told lies saying that Yahweh [MTY] gave those messages to you, so you must be executed.’ [So] if someone prophesies [like that], his own father and mother must stab him [and kill him].
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
At that time, the false prophets will be ashamed [that they claimed to have received messages from me in] their visions and prophesies [that they told to people]. They will no [longer] deceive people by wearing the clothes [that prophets usually wear], clothes made of [animals’] hair.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
[So] each of them will say, ‘I am not [really] a prophet; I am a farmer, and I have been a farmer on my land ever since I was a boy!’
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
But someone, [seeing the wounds on one of those prophet’s bodies, will suspect that he injured himself during rituals to worship idols, and he] will ask ‘Why are those wounds on your body?’ And he [will lie, saying] ‘I was injured [when I was] at my friend’s house.’”
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
The Commander of the armies of angels says, “[My] sword [APO] must strike [the one who is like] [MET] my shepherd, the man who is (my companion/very (close/dear) to me). When the shepherd is killed, [those who are like] [MET] his sheep will scatter. [And those who are like] [MET] my little sheep will [also] be attacked [IDM].”
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Yahweh [also] says, “Two-thirds [of the people in Judah] will die [DOU]. [Only] one-third [of the people in Judah] will remain alive.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
And I will test the ones that remain alive [by causing them to experience great difficulties, to find out if they will continue to worship me]. I will purify them like [MET] a man purifies gold or silver by putting it into a [very hot] fire. [Then] my people will call to me [MTY] [for help], and I will answer them. I will say [to them], ‘You are my people,’ and they will say, ‘Yahweh is our God.’”

< Zakariya 13 >