< Zakariya 13 >
1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
On that day shall there be a fountain opened to the house of David and to the inhabitants of Jerusalem, for cleansing from sin and for purification.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
And it shall come to pass on that day, saith the Lord of hosts, that I will cut off the names of the idols out of the land, and they shall not be remembered any more: and also the prophets and the unclean spirit will I remove out of the land.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
And it shall come to pass, if any one should yet prophesy, that his father and his mother who have begotten him shall say unto him, Thou shalt not live; for falsely hast thou spoken in the name of the Lord: and his father and his mother who have begotten him shall thrust him through when he prophesieth.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
And it shall come to pass on that day, that the prophets shall be ashamed every one because of his vision, when he prophesieth; and they shall not clothe themselves with a hairy cloak in order to deceive.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
But he will say, I am no prophet, a man that tilleth the ground am I; for some one hath taught me to keep cattle from my youth.
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
And should some one say unto him, What are these wounds between thy hands? Then will he say, Those with which I have been wounded in the house of my [vicious] friends.
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
Awake, O sword, against my shepherd, and against the man whom I have associated with me, saith the Lord of hosts: smite the shepherd, and the sheep shall be scattered; but I will turn my hand toward the feeble ones.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
And it shall come to pass, that in all the land, saith the Lord, two parts [of those] therein shall be cut off, shall perish; but the third part shall be left therein.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
And I will bring the third part into the fire, and I will refine them as one refineth silver, and will probe them as gold is probed: they will call on my name, and I will answer their prayer; I will say, They arc my people; and they will say, The Lord is my God.