< Zakariya 13 >
1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
Paa hin Dag skal en Kilde vælde frem for Davids Hus og Jerusalems Indbyggere mod Synd og Urenhed.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
Og paa hin Dag, lyder det fra Hærskarers HERRE, udrydder jeg Afgudernes Navne af Landet, saa de ikke mer skal ihukommes; ogsaa Profeterne og Urenhedens Aand driver jeg ud af Landet.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
Naar nogen da atter profeterer, skal hans egne Forældre, hans Fader og Moder, sige til ham: »Du har forbrudt dit Liv, thi du har talt Løgn i HERRENS Navn.« Og hans egne Forældre, hans Fader og Moder, skal gennembore ham, naar han profeterer.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
Paa hin Dag skal hver en Profet skamme sig over sine Syner, naar han profeterer, og han skal ikke klæde sig i laadden Kappe for at føre Folk bag Lyset,
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
men sige: »Jeg er ingen Profet; jeg er Bonde og har dyrket Jord fra min Ungdom.«
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
Og spørger man ham: »Hvad er det for Saar paa dit Bryst?« skal han sige: »Dem fik jeg i mine Boleres Hus.«
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
Frem, Sværd, imod min Hyrde, mod Manden, som staar mig nær, saa lyder det fra Hærskarers HERRE. Hyrden vil jeg slaa, saa Faarehjorden spredes; mod Drengene løfter jeg Haanden.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Og i hele Landet lyder det fra HERREN, skal to Tredjedele udryddes og udaande, men een Tredjedel skal levnes.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
Og denne Tredjedel fører jeg i Ild og renser den, som man renser Sølv, prøver den, som man prøver Guld. Den skal paakalde mit Navn, og jeg svarer; jeg siger: »Den er mit Folk.« Og den skal sige: »HERREN er min Gud.«