< Zakariya 13 >
1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
Paa den Dag skal der være en aabnet Kilde for Davids Hus og for Jerusalems Indbyggere imod Synd og imod Urenhed.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
Og det skal ske paa den Dag, siger den Herre Zebaoth, at jeg vil udrydde Afgudernes Navne af Landet, og de skulle ikke ihukommes ydermere; ogsaa Profeterne og den urene Aand vil jeg lade forsvinde af Landet.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
Og det skal ske, naar nogen spaar ydermere, da skal hans Fader og hans Moder, som avlede ham, sige til ham: Du skal ikke leve, thi du har talt Løgn i Herrens Navn; og hans Fader og hans Moder, som avlede ham, skulle gennembore Ham, naar han spaar.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
Og det skal ske paa den Dag, da skulle Profeterne skamme sig, hver over sit Syn, naar han spaar; og de skulle ikke iføre sig en laadden Kappe for at bedrage.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
Men han skal sige: Jeg er ingen Profet, jeg er en Agerdyrker; thi en Mand har købt mig fra min Ungdom af.
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
Og dersom nogen siger til ham: Hvad betyde disse Saar i dine Hænder? da skal han sige: Det er Slag, som jeg har faaet i deres Hus, som elskede mig.
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
Sværd! vaagn op imod min Hyrde og imod den Mand, som er min Næste, siger den Herre Zebaoth; slaa Hyrden, og Faarene skulle adspredes, og jeg vil føre min Haand tilbage over de smaa.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
Og det skal ske i alt Landet, siger Herren: De to Dele, som ere derudi, skulle udryddes, de skulle opgive Aanden; men den ene Tredjedel skal blive tilbage derudi.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
Og jeg vil bringe denne Tredjedel i Ilden og lutre den, som man lutrer Sølvet, og prøve den, som man prøver Guldet; den skal paakalde mit Navn, og jeg vil bønhøre den; jeg siger: Det er mit Folk, og den skal sige: Herren er min Gud.