< Zakariya 12 >
1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
Uma revelação da palavra de Iavé a respeito de Israel: Javé, que estende os céus e lança os alicerces da terra, e forma o espírito do homem dentro dele diz:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
“Eis que farei de Jerusalém um cálice de roda para todos os povos vizinhos, e será também sobre Judá no cerco contra Jerusalém.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
Acontecerá nesse dia que farei de Jerusalém uma pedra pesada para todos os povos. Todos os que se sobrecarregarem com ela serão gravemente feridos, e todas as nações da terra serão reunidas contra ela.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
Naquele dia”, diz Yahweh, “eu atacarei cada cavalo com terror e seu cavaleiro com loucura”. Abrirei meus olhos sobre a casa de Judá, e baterei em todos os cavalos dos povos com cegueira”.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Os chefes de Judá dirão em seu coração: “Os habitantes de Jerusalém são minha força em Iavé dos Exércitos seu Deus”.
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
Naquele dia farei os chefes de Judá como uma panela de fogo entre lenha, e como uma tocha flamejante entre feixes. Eles devorarão todos os povos vizinhos à direita e à esquerda; e Jerusalém habitará mais uma vez em seu próprio lugar, mesmo em Jerusalém.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
Yahweh também salvará primeiro as tendas de Judá, que a glória da casa de Davi e a glória dos habitantes de Jerusalém não sejam ampliadas acima de Judá.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
Naquele dia, Javé defenderá os habitantes de Jerusalém. Aquele que for fraco entre eles naquele dia será como Davi, e a casa de Davi será como Deus, como o anjo de Javé diante deles.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
Acontecerá naquele dia, que procurarei destruir todas as nações que vierem contra Jerusalém.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
derramarei sobre a casa de Davi e sobre os habitantes de Jerusalém o espírito de graça e de súplica. Eles olharão para mim quem trespassaram; e chorarão por ele como se chorasse por seu único filho, e chorarão amargamente por ele como se chorasse por seu primogênito.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
Naquele dia haverá um grande luto em Jerusalém, como o luto de Hadadrimmon no vale de Megiddo.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
A terra chorará, cada família à parte; a família da casa de Davi à parte, e suas esposas à parte; a família da casa de Natã à parte, e suas esposas à parte;
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
a família da casa de Levi à parte, e suas esposas à parte; a família dos Shimeítas à parte, e suas esposas à parte;
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
todas as famílias que permanecerem, cada família à parte, e suas esposas à parte.