< Zakariya 12 >

1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
این است پیام خداوند برای اسرائیل. خداوند که آسمانها را گسترانید و بنیاد زمین را نهاد و روح انسان را در درونش قرار داد، چنین می‌گوید:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
«اورشلیم را برای قومهای همسایه که سپاهیان خود را برای محاصرهٔ اورشلیم و سایر شهرهای یهودا می‌فرستند، مثل جامی سرگیجه‌آور می‌سازم.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
هنگامی که تمام قومهای جهان بر ضد اورشلیم جمع شوند، من اورشلیم را برای آنها مانند سنگ عظیمی خواهم ساخت، که هر کس بخواهد آن را تکان دهد خود سخت مجروح شود.»
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
خداوند می‌فرماید: «در آن روز، همۀ اسبان را به گیجی و همۀ سوارانشان را به جنون دچار خواهم کرد. من مراقب خاندان یهودا خواهم بود، اما اسبان دشمنانشان را به کوری مبتلا خواهم ساخت.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
آنگاه رهبران یهودا در دل خود خواهند گفت: مردم اورشلیم قوی هستند، زیرا خداوند لشکرهای آسمان، خدای ایشان است.
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
«در آن روز، رهبران یهودا را مثل شعلۀ آتشی که جنگلها و مزارع را می‌سوزاند، می‌گردانم. آنها تمام قومهای همسایه را از راست و چپ خواهند سوزاند، و مردم اورشلیم در امنیت خواهند بود.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
«خداوند سایر شهرهای یهودا را پیش از اورشلیم پیروز می‌گرداند تا مردم اورشلیم و نسل سلطنتی داوود از پیروزی خود مغرور نشوند.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
«در آن روز خداوند از مردم اورشلیم دفاع خواهد کرد. ضعیفترین آنها مثل داوود پادشاه قوی خواهد بود، و نسل سلطنتی داوود مانند خدا و مثل فرشتهٔ خداوند در پیشاپیش آنها حرکت خواهند کرد!
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
زیرا قصد من این است که تمام قومهایی را که به جنگ اورشلیم می‌آیند نابود کنم.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
«من روح فیض و دعا را بر خاندان داوود و بر ساکنان اورشلیم خواهم ریخت، و آنها بر من که نیزه زده‌اند خواهند نگریست و عزاداری خواهند نمود چنانکه گویی برای تنها فرزند خود عزا گرفته‌اند، و آنچنان ماتم خواهند گرفت که گویی پسر ارشدشان مرده است.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
در آن روز، در اورشلیم ماتم بزرگی بر پا خواهد شد همانند ماتم عظیمی که برای هَدَد رِمّون در وادی مجدون بر پا نمودند.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
تمامی این سرزمین سوگواری خواهد کرد، هر طایفه‌ای جداگانه: طایفۀ خاندان داوود جداگانه، و زنانشان جداگانه؛ طایفۀ خاندان ناتان جداگانه، و زنانشان جداگانه؛
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
طایفۀ خاندان لاوی جداگانه، و زنانشان جداگانه؛ طایفۀ شِمعی جداگانه، و زنانشان جداگانه؛
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
و همۀ طایفه‌های باقیمانده، هر یک جداگانه، و زنانشان جداگانه.

< Zakariya 12 >