< Zakariya 12 >
1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
[This is] a message from Yahweh concerning Israel. Yahweh is the one who stretched out the sky, who created the earth, and who (gave life to humans/caused humans to be alive). This is what he says:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
“I will soon cause Jerusalem to be [like] [MET] a cup full [of very strong alcoholic drink], and the people of other nations who drink it will stagger around. And they will come and attack Jerusalem and [the other towns in] Judah.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
At that time, [the armies of] all the nations will gather to attack Jerusalem, but I will cause [the leaders of] Judah to be [like] [SIM] a very heavy rock, and all who [try to] lift it will be badly injured.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
At that time I will cause every [one of their enemies’] horses to panic, and their riders to become crazy. I [IDM] will protect the people of Judah, but I will cause all their enemies’ horses to become blind.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Then the leaders of Judah will say to themselves, ‘The people in Jerusalem are strong because the Commander of the armies of angels is their God.’
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
At that time I will enable the leaders of Judah to be like [SIM] a pan containing hot coals [that is put] in a woodpile [to set it on fire], or like [SIM] a burning torch [that is put] in a [field of] ripe grain [to set it on fire]. The leaders of Judah [and their army] will destroy the people of the surrounding nations in all directions. But [the people of] Jerusalem will remain safe.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
And [I], Yahweh, will protect the tents of [the soldiers in other places in] Judah before [I rescue the people of Jerusalem], in order that the leaders of Jerusalem [DOU] will not be honored more than [the people in other places in] Judah [are honored].
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
At that time, I will protect [MET] the people of Jerusalem. When that happens, even the weakest people in Jerusalem will be [strong] like [King] David [was]. And the descendants [MTY] of David will [rule the people] like I [would], as though an angel sent from [me], Yahweh, was their leader.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
At that time, I will prepare to destroy all the nations that attack Jerusalem.”
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
“I, [Yahweh, ] will cause the descendants [MTY] of [King] David to act very kindly and mercifully. They will look at me, [the one] who has been stabbed, and they will cry bitterly, like people cry for a firstborn son [who has died] [DOU].
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
At that time, many people in Jerusalem will be crying bitterly, like people cried [when King Josiah was killed in the battle] at Hadad-Rimmon on the Megiddo Plain.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
Many people in Judah will cry, each family by themselves: the male descendants of David by themselves, and their wives by themselves, the male descendants of [David’s son] Nathan by themselves, and their wives by themselves,
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
the male descendants [MTY] of Levi by themselves, and their wives by themselves, the male descendants of [Levi’s grandson] Shimei by themselves, and their wives by themselves,
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
and all the other members [of the kings’ clans and the priests’ clans] by themselves, and their wives by themselves.”