< Zakariya 12 >

1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
The prophecy of the word of Jehovah concerning Israel. Thus saith Jehovah, who stretched out the heavens, And laid the foundation of the earth, And formed the spirit of man within him:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
Behold, I make Jerusalem a cup of giddiness to all the nations round about, And for Judah also shall it be In the siege against Jerusalem.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
And in that day will I make Jerusalem A burdensome stone for all nations; All that lift it up shall tear themselves, And all the nations of the earth shall gather themselves together against it.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
In that day, saith Jehovah, I will smite every horse with amazement, And his rider with madness; I will open mine eyes upon the house of Judah, And every horse of the nations will I smite with blindness.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Then shall the leaders of Judah say in their heart, “Strong are the inhabitants of Jerusalem, Through Jehovah of hosts, their God.”
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
In that day will I make the leaders of Judah Like a fire-pan among wood, And like a torch of fire in a sheaf, And they shall devour, on the right hand and on the left, All the nations round about. And Jerusalem shall again dwell in her own place at Jerusalem.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
Jehovah will also save the tents of Judah first, That the glory of the house of David, And the glory of the inhabitants of Jerusalem, May not magnify itself against Judah.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
In that day shall Jehovah defend the inhabitants of Jerusalem, And he that is feeble among them in that day shall be like David, And the house of David shall be as God, As the angel of Jehovah before them.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
And it shall come to pass in that day That I will seek to destroy all the nations Which come against Jerusalem.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
Then will I pour upon the house of David, And upon the inhabitants of Jerusalem, A spirit of supplication, and of prayer; And they shall look to me whom they pierced, And they shall mourn for him, as one mourneth for his only son, And shall be in bitterness for him, as one that is in bitterness for his first-born.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
In that day the mourning shall be great in Jerusalem, As the mourning of Hadadrimmon in the valley of Megiddo.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
And the land shall mourn, every family apart; The family of the house of David apart, and their wives apart; The family of the house of Nathan apart, and their wives apart;
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
The family of the house of Levi apart, and their wives apart; The family of the house of Shimei apart, and their wives apart;
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
All the families that remain, Every family apart, and their wives apart.

< Zakariya 12 >