< Zakariya 12 >

1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
A prophecy: This message came from the Lord concerning Israel, a declaration of the Lord who spread out the heavens, who laid the foundations of the earth, and who placed the breath of life within human beings.
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
Look! I am going to make Jerusalem like a cup containing alcoholic drink that will make all the surrounding nations stagger like drunks when they come to attack Judah and Jerusalem.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
On that day I will make Jerusalem like a heavy rock to all peoples. Anyone who tries to lift the rock will injure themselves badly. All the nations will join together to attack Jerusalem.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
On that day I will make every horse panic-stricken and every rider go mad, declares the Lord, but I will watch over the people of Judah while I blind all the horses of their enemies.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Then the families of Judah will say to themselves, the people of Jerusalem are strong in their God, the Lord Almighty.
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
On that day I will make the families of Judah like burning coals in a wood, like a flaming torch in a field of straw. They will burn up to the right and to the left all the surrounding peoples, while the people of Jerusalem will live safely in their city.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
The Lord will give the victory to the soldiers of Judah first so that the glory of the house of David and the glory of the inhabitants of Jerusalem shall not be greater than that of Judah.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
On that day the Lord will place a shield around the people of Jerusalem so that even the clumsiest of them will be as skilled a warrior as David, and the house of David will be like God, like the angel of the Lord who leads them.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
On that day I will start destroying all those nations that attack Jerusalem.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
I will pour out a spirit of grace and prayer on the house of David and the inhabitants of Jerusalem. They will look at me whom they pierced, and they will wail in grief over him, mourning as for an only child, weeping bitterly as for a firstborn.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
On that day the mourning in Jerusalem will be as great as the mourning in Hadad-Rimmon in the valley of Megiddo.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
The land will mourn, every family alone: the family house of David alone and their women by themselves, the families of Nathan,
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
Levi, and Shimei—
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
and all the surviving families and their women, each group mourning alone by themselves.

< Zakariya 12 >