< Zakariya 12 >
1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
The word of the Lord about Israel. The Lord by whom the heavens are stretched out and the bases of the earth put in place, and the spirit of man formed inside him, has said:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
See, I will make Jerusalem a cup of shaking fear to all the peoples round about, when Jerusalem is shut in.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
And it will come about in that day that I will make Jerusalem a stone of great weight for all the peoples; all those who take it up will be badly wounded; and all the nations of the earth will come together against it.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
In that day, says the Lord, I will put fear into every horse and make every horseman go off his head: and my eyes will be open on the people of Judah, and I will make every horse of the peoples blind.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
And the families of Judah will say in their hearts, The people of Jerusalem have their strength in the Lord of armies, their God.
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
In that day I will make the families of Judah like a pot with fire in it among trees, and like a flaming stick among cut grain; they will send destruction on all the peoples round about, on the right hand and on the left: and Jerusalem will be living again in the place which is hers, that is, in Jerusalem.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
And the Lord will give salvation to the tents of Judah first, so that the glory of the family of David and the glory of the people of Jerusalem may not be greater than that of Judah.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
In that day the Lord will be a cover over the people of Jerusalem; and he who is feeble among them in that day will be as strong as David, and the family of David will be as God, as the angel of the Lord before them.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
And it will come about on that day that I will take in hand the destruction of all the nations who come against Jerusalem.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
And I will send down on the family of David and on the people of Jerusalem the spirit of grace and of prayer; and their eyes will be turned to the one who was wounded by their hands: and they will be weeping for him as for an only son, and their grief for him will be bitter, like the grief of one sorrowing for his oldest son.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
In that day there will be a great weeping in Jerusalem, like the weeping of Hadad-rimmon in the valley of Megiddon.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
And the land will give itself to weeping, every family separately; the family of David by themselves, and their wives by themselves; the family of Nathan by themselves, and their wives by themselves;
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
The family of Levi by themselves, and their wives by themselves; the family of Shimei by themselves, and their wives by themselves;
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
And all the other families by themselves, and their wives by themselves.