< Zakariya 12 >
1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
Et Udsagn; HERRENs Ord om Israel. Det lyder fra HERREN; som udspændte Himmelen, grundfæstede Jorden og dannede Menneskets Ånd i dets Indre:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
Se, jeg gør Jerusalem til et berusende Bæger for alle Folkeslag trindt om; også Juda skal være med til at belejre Jerusalem.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
På hin Dag gør jeg Jerusalem til Løftesten for alle Folkeslag - enhver, som løfter den, skal rive sig på den! Og alle Jordens Folk skal samle sig imod det.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
På hin Dag, lyder det fra HERREN, slår jeg alle Heste med Angst og Rytterne med Vanvid; Judas Hus åbner jeg Øjnene på, men alle Folkeslagene slår jeg med Blindhed.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Og Judas Stammer skal tænke: "Jerusalems Indbyggere er stærke i Hærskarers HERRE, deres Gud."
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
På hin Dag gør jeg Judas Stammer til en Ildgryde mellem Brændestykker, et brændende Blus mellem Neg, og de skal æde til højre og venstre alle Folkeslag trindt om, og Jerusalem bliver roligt på sit Sted, i Jerusalem.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
Så giver HERREN først Judas Telte Sejr, for at Davids Hus og Jerusalems Indbyggere ikke skal vinde større Ry end Juda.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
På hin Dag værner HERREN om Jerusalems Indbyggere, og den skrøbeligste iblandt dem skal på hin Dag blive som David, men Davids Hus som Gud, som HERRENs Engel foran dem.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
På hin Dag vil jeg søge at tilintetgøre alle de Folk, som kommer imod Jerusalem.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
Og så udgyder jeg over Davids Hus og Jerusalems Indbyg- gere Nådens og Bønnens Ånd, så de ser hen til ham, de har gennemstunget, og sørger over ham, som man sørger over en enbåren Søn, og holder Klage over ham, son1 man holder Klage over den førstefødte.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
På hin Dag skal Sorgen blive stor i Jerusalem som Sorgen over Hadadrimmon i Megiddos Dal.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
Landet skal sørge, hver Slægt for sig, Davids Hus's Slægt for sig og deres Kvinder for sig, Natans Hus's Slægt for sig og deres Kvinder for sig,
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
Levis Hus's Slægt for sig og deres Kvinder for sig, Sjim'iternes Slægt for sig og deres Kvinder for sig,
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
alle de tiloversblevne Slægter hver for sig og deres Kvinder for sig.