< Zakariya 11 >

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
Ouvre tes portes, ô Liban! Que le feu exerce ses ravages parmi tes cèdres!
2 Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
Lamente-toi, cyprès, car le cèdre est tombé, les fiers géants sont abattus! Lamentez-vous, chèvres de Basan, car elle est à terre, la forêt si riche en fruits!
3 Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
On entend les sanglots des pasteurs, car leur splendeur est détruite; on entend les rugissements des lions, car les massifs du Jourdain sont ravagés.
4 Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
Ainsi parle l’Eternel, mon Dieu: "Mène paître ces brebis destinées à la boucherie,
5 Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
puisque leurs acquéreurs les égorgent, sans se croire en faute, et ceux qui les vendent s’écrient: "Dieu soit loué! J’Ai fait fortune!" Et leurs pasteurs ne les épargnent point.
6 Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
C’Est que désormais je n’aurai plus de ménagement pour les habitants de ce pays, dit l’Eternel; je vais, au contraire, livrer ces hommes aux entreprises de l’un sur l’autre et au pouvoir de leur roi. Ils couvriront le pays de ruines, et je ne le sauverai pas de leurs mains."
7 Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
Je menai donc paître ces brebis destinées à la boucherie, à savoir les plus faibles du troupeau; et je me munis de deux bâtons, dont j’appelai l’un "Bienveillance" et l’autre "Liens". Tandis que je faisais paître les brebis,
8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
et anéantissais les trois pasteurs en un seul mois, ma patience se lassa à leur égard, et elles aussi en eurent assez de moi.
9 na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
Et je dis: "Je ne veux plus vous paître. Périsse celle qui doit périr, succombe celle qui doit succomber, et que celles qui restent se dévorent l’une l’autre!"
10 Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
Puis, je pris mon bâton "Bienveillance" et le brisai, afin de rompre mon alliance que j’avais conclue avec toutes les nations.
11 An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
Elle fut ainsi rompue ce jour-là, et elles reconnurent bien, les plus humbles du troupeau qui me voyaient faire, que c’était la parole de l’Eternel.
12 Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
Je leur dis: "Si tel est votre bon plaisir, donnez-moi mon salaire, et sinon, laissez-le!" Alors ils me comptèrent mon salaire, trente pièces d’argent.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
Et l’Eternel me dit: "Jette-le au Trésor, ce prix magnifique auquel j’ai été estimé par eux, et je pris les trente pièces d’argent et les jetai au Trésor, dans la maison de l’Eternel.
14 Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
Puis je mis en pièces mon second bâton "Liens", afin d’abolir la fraternité entre Juda et Israël.
15 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
L’Eternel me dit: "Munis toi encore du baggage d’un pasteur idiot.
16 Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
Car voici, je vais établir un pasteur en ce pays, qui ne saura pas soigner les brebis en perdition, rechercher celle qui s’égare étourdiment, guérir celle qui a une fracture, nourrir celle qui est intacte, mais qui consommera la chair des plus grasses et leur brisera les ongles.
17 “Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”
Oh! malheur au pasteur de néant qui délaisse son troupeau! Que la sécheresse atteigne son bras et son œil droit! Que son bras soit complètement paralysé et son œil droit tout à fait éteint!"

< Zakariya 11 >