< Zakariya 11 >

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
Ouvrez vos portes, Liban, pour que le feu dévore vos cèdres.
2 Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
Gémis, cyprès, car le cèdre est tombé, parce que les majestueux sont détruits. Gémissez, chênes de Bashan, car la forêt forte est tombée.
3 Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
La voix des pleurs des bergers! Car leur gloire est détruite - une voix qui ressemble au rugissement de jeunes lions! Car la fierté du Jourdain est ruinée.
4 Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
Yahvé, mon Dieu, dit: « Paisez le troupeau de la boucherie.
5 Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
Leurs acheteurs les égorgent et restent impunis. Ceux qui les vendent disent: « Béni soit Yahvé, car je suis riche », et leurs propres bergers n'ont pas pitié d'eux.
6 Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
Car je n'aurai plus pitié des habitants du pays, dit l'Éternel, mais voici que je livrerai chacun de ces hommes entre les mains de son prochain et entre les mains de son roi. Ils frapperont le pays, et de leur main je ne les délivrerai pas. »
7 Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
J'ai donc nourri le troupeau à abattre, surtout les opprimés du troupeau. Je pris pour moi deux bâtons. J'appelai l'un « faveur » et l'autre « union », et je fis paître le troupeau.
8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
J'exterminai les trois bergers en un mois, car mon âme était lasse d'eux, et leur âme aussi me haïssait.
9 na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
Alors je dis: « Je ne vous ferai pas paître. Ce qui meurt, qu'il meure; et ce qui doit être retranché, qu'il soit retranché; et que ceux qui restent mangent la chair les uns des autres. »
10 Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
Je pris mon bâton Favor et je le taillai en pièces, afin de rompre l'alliance que j'avais conclue avec tous les peuples.
11 An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
Elle fut rompue ce jour-là, et les pauvres du troupeau qui m'écoutaient surent que c'était la parole de Yahvé.
12 Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
Je leur dis: « Si vous le jugez bon, donnez-moi mon salaire; sinon, gardez-le. » Ils pesèrent donc pour mon salaire trente pièces d'argent.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
L'Éternel me dit: « Jette-les au potier, c'est le beau prix auquel ils m'ont estimé. » J'ai pris les trente pièces d'argent et je les ai jetées au potier dans la maison de l'Éternel.
14 Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
Puis j'ai coupé mon autre bâton, l'Union, afin de rompre la fraternité entre Juda et Israël.
15 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
L'Éternel me dit: « Prends encore pour toi l'équipement d'un berger insensé.
16 Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
Car voici que je vais susciter dans le pays un berger qui ne visitera pas ceux qui sont retranchés, ne cherchera pas ceux qui sont dispersés, ne guérira pas ceux qui sont brisés et ne nourrira pas ceux qui sont sains; mais il mangera la viande des brebis grasses et mettra leurs sabots en pièces.
17 “Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”
Malheur au berger sans valeur qui abandonne le troupeau! L'épée frappera son bras et son œil droit. Son bras sera complètement desséché, et son œil droit sera complètement aveuglé! ».

< Zakariya 11 >