< Zakariya 11 >

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
[You people of] [APO] Lebanon [should] open your gates, [because you will not be able to stop] fire from burning your cedar [trees]!
2 Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
Your cypress/pine [trees] [APO] should [also] wail because the cedar [trees] have been cut down. Those glorious/great trees have been destroyed. The oak trees in the Bashan [region] should also wail, because the other trees in the forest have been cut down.
3 Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
And listen to the shepherds crying because the fertile pastures have been ruined. Listen to the lions roar; they roar because the delightful forest [where they live] near the Jordan [River] has been ruined.
4 Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
This is what Yahweh my God said [to me]: “[I want you to] become a shepherd for a flock [of sheep that are about] to be slaughtered.
5 Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
The people who are going to buy the sheep will kill the sheep, and they will not be punished. Those who are selling the sheep say, ‘[I] praise Yahweh, [because] I will become rich!’ Even the shepherds do not feel sorry for the sheep.
6 Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
And similarly, I no longer feel sorry for the people of this country. I am going to allow many of them [HYP] to be captured by other people or by their king. Those who capture them will ruin this country, and I will not rescue any [of the people].”
7 Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
So I became the shepherd of a flock [of sheep that were about] to be slaughtered [for their meat to be sold] to the dealers. [I took good care of the sheep, even the ones that were the weakest sheep. Then] I took two [shepherds’] /walking sticks). I named the one [staff] ‘Kindness’ and the other [staff] ‘Union’. And I took good care of the sheep.
8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
But the three shepherds [who had been working with me] detested me, and I became impatient with them. Within one month I (dismissed/got rid of) those shepherds.
9 na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
So I said [to the dealers], “I will no [longer] be the shepherd. I will allow the ones that are dying to die. I will allow the ones that are getting lost to get lost. And I will not prevent those that remain from destroying each other.”
10 Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
Then I took the staff that I had named ‘Kindness’ and I broke it. [That showed that Yahweh] was annulling/canceling the agreement that he had made with all the people-groups.
11 An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
So that agreement was ended immediately. And the men who bought and sold sheep who were watching me knew [by seeing what I was doing] that I was giving them a message from Yahweh.
12 Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
I told them, “If you think it is what you should do, pay me [for taking care of the sheep]. If you do not think that is what you should do, do not pay me.” So they paid me [only] 30 pieces of silver.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
Then Yahweh said to me, “[That is a ridiculously small amount of money that they have paid you]! [So] throw it to the man who makes clay pots!” So I took the silver to the temple of Yahweh, and I threw it in the chest where the offerings/money is kept.
14 Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
Then I broke my second staff, [the one that I named] ‘Union’. That [indicated that] Judah and Israel would no longer be united.
15 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
Then Yahweh said to me, “Take again the things that a foolish shepherd uses,
16 Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
because I am going to appoint a new king for the people, [one who will not take care of my people. He will be like a foolish shepherd]: [MET] He will not take care of those who are dying, those who are very young, those who have been injured, or those who do not have enough food. Instead, he will [treat them very cruelly, like a shepherd who would] [MET] kill and eat the best sheep and tear off their hoofs.
17 “Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”
But terrible things will happen to that foolish/useless king who abandons the people [MET] over whom he rules. [His enemies] will strike his arm and his right eye with their swords. [The result will be that] he will have no strength in his arm, and his right eye will become completely blind.”

< Zakariya 11 >