< Zakariya 11 >

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
Open, O Lebanon, thy doors, —that a fire, may devour, thy cedar,
2 Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
Howl, fir-tree, for fallen is the cedar, because, the majestic ones, are spoiled: howl, ye oaks of Bashan, for the inaccessible forest, hath come down.
3 Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
The noise of the howling of the shepherds, for spoiled is their majesty, —The noise of the roaring of the young lions, for spoiled are the proud banks of the Jordan.
4 Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
Thus, saith Yahweh my God, —Tend thou the flock doomed to slaughter:
5 Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
Whose, buyers, slay them, and are not held guilty, and whose, sellers, say—Blessed be Yahweh, that I am become rich, And so, their own shepherds, have no pity upon them.
6 Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
Surely I will have pity no longer upon the inhabitants of the earth, Declareth Yahweh, —Therefore lo! I am delivering up mankind, every man into the hand of his neighbour, and into the hand of his king, and they will crush the earth, nor will I deliver out of their hand.
7 Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
So I tended the flock doomed to slaughter, for the sheep-merchants, —and took unto me two staves, the one, I called Grace, and, the other, I called Union, thus I tended the sheep,
8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
And I sent off three shepherds, in one month, —for impatient was my soul with them, moreover also, their soul, felt a loathing against me.
9 na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
Then said I—I will not tend you, —the dying, may die, and, the disappearing, may disappear, and, the remainder, may devour one another.
10 Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
So I took my staff Grace, and cut it in two, —that I might set aside my covenant which I had solemnised with all the peoples.
11 An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
When it was broken, on that day, then did the sheep- merchants who were watching me, know, that, the word of Yahweh, it was.
12 Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
Then said I unto them, If it be good in your eyes, give me my wage, and, if not, forbear. So they weighed out my wage, thirty pieces of silver.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
Then said Yahweh unto me, Cast it into the treasury, the magnificent price at which I had been valued by them! So I took the thirty pieces of silver, and cast them, in the house of Yahweh, into the treasury.
14 Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
Then cut I in two my second staff, even Union, —that I might break the brotherhood between Judah and Israel.
15 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
Then said Yahweh unto me, —Yet further take thee the implements of a worthless shepherd.
16 Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
For lo! I am raising up a shepherd in the land, the disappearing, will he not visit, the straying, will he not seek, and, the fractured, will he not bind up, —the weak, will he not nourish, but, the flesh of the fat, will he eat, and, their hoofs, will he break in pieces.
17 “Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”
Alas! for my worthless shepherd, who forsaketh the flock, A sword upon his arm, and upon his right eye!—his arm, shall be, utterly withered, and, his right eye, shall be, wholly darkened.

< Zakariya 11 >