< Zakariya 11 >

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.
Libanon, luk Dørene op, saa Ild kan fortære dine Cedre!
2 Yi kuka, ya itacen fir, gama itacen al’ul ya fāɗi; itatuwa masu daraja sun lalace! Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan; an sassare itatuwan babban kurmi!
Klag, Cypres, thi Cedren er faldet, de ædle Træer lagt øde! Klag, I Basans Ege, thi Fredskoven ligger fældet!
3 Ku ji kukan makiyaya; an ɓata musu wuraren kiwonsu masu ciyayi! Ku ji rurin zakoki; an lalatar da jejin Urdun!
Hør, hvor Hyrderne klager, thi deres Græsgang er hærget; hør, hvor Løverne brøler, thi Jordans Tykning er hærget.
4 Ga abin da Ubangiji Allahna ya ce, “Yi kiwon garken tumakin da za a yanka.
Saaledes sagde HERREN min Gud: Røgt Slagtefaarene,
5 Masu sayensu sun yanyanka su, suka kuwa tafi ba hukunci. Masu sayar da su sun ce, ‘Yabi Ubangiji, na yi arziki!’ Makiyayansu ma ba su ji tausayinsu ba.
hvis Køber slagter dem uden at føle Skyld, og hvis Sælger siger: »HERREN være lovet, jeg blev rig.« Og deres Hyrder sparer dem ikke.
6 Gama ba zan ƙara jin tausayin mutanen ƙasar ba,” in ji Ubangiji. “Zan ba da kowa ga maƙwabcinsa da kuma sarkinsa. Za su zalunci ƙasar, ba zan kuma cece su daga hannuwansu ba.”
(Thi jeg vil ikke længer spare Landets Indbyggere, lyder det fra HERREN; men se, jeg lader hvert Menneske falde i sin Hyrdes og sin Konges Haand; og de skal ødelægge Landet, og jeg vil ingen redde af deres Haand).
7 Saboda haka na yi kiwon garken da za a yanka, musamman garken da ake zalunta. Sai na ɗauki sanduna biyu na kira ɗaya Tagomashi, ɗaya kuma Haɗinkai, sai na yi kiwon garken.
Saa røgtede jeg Slagtefaarene for Faareprangerne og tog mig to Stave; den ene kaldte jeg »Liflighed«, den anden »Baand«; og jeg røgtede Faarene.
8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su
(Og jeg ryddede de tre Hyrder af Vejen i een Maaned). Saa tabte jeg Taalmodigheden med dem, og de blev ogsaa kede af mig.
9 na ce, “Ba zan zama makiyayinku ba. Bari masu mutuwa su mutu, masu hallaka kuma su hallaka. Bari waɗanda suka ragu su ci naman juna.”
Og jeg sagde: »Jeg vil ikke røgte eder; lad dø, hvad dø skal, lad bortkomme, hvad bortkomme skal, og lad de andre æde hverandres Kød!«
10 Sai na ɗauki sandana mai suna Tagomashi na karya shi, na janye alkawarin da na yi da dukan al’ummai.
Saa tog jeg Staven, som hed »Liflighed«, og sønderbrød den for at bryde den Overenskomst, jeg havde sluttet (med alle Folkeslag;
11 An janye shi a ranan nan, saboda haka garken da yake cikin wahala masu kallona sun san cewa maganar Ubangiji ce.
og den blev brudt samme Dag, og Faareprangerne, som holdt Øje med mig, kendte, at det var HERRENS Ord).
12 Na faɗa musu cewa, “In kun ga ya fi kyau, ku biya ni; in kuwa ba haka ba, ku riƙe.” Saboda haka suka biya ni azurfa talatin.
Og jeg sagde til dem: »Om I synes, saa giv mig min Løn; hvis ikke, saa lad være!« Saa afvejede de min Løn, tredive Sekel Sølv.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Jefar da shi cikin ma’aji,” Lada mai kyau da aka yi cinikina ne! Saboda haka sai na ɗauki azurfa talatin ɗin na jefa su cikin gidan Ubangiji don a sa cikin ma’aji.
Men HERREN sagde til mig: »Kast den til Pottemageren, den dejlige Pris, de har vurderet mig til!« Og jeg tog de tredive Sekel Sølv og kastede dem til Pottemageren i HERRENS Hus.
14 Sai na karya sandana na biyu mai suna Haɗinkai, ta haka na karya’yan’uwantakar da take tsakanin Yahuda da Isra’ila.
Saa sønderbrød jeg den anden Hyrdestav »Baand« for at bryde Broderskabet imellem Juda og Jerusalem.
15 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na wawan makiyayi.
Siden sagde HERREN til mig: Udstyr dig atter som en Hyrde, en Daare af en Hyrde!
16 Gama zan tā da makiyayi a ƙasar wanda ba zai kula da ɓatattu, ko yă nemi ƙanana, ko yă warkar da waɗanda suka ji ciwo, ko kuma ciyar da masu lafiya ba, sai dai zai ci naman keɓaɓɓun tumaki, yă farfasa kofatonsu.
(Thi se, jeg lader en Hyrde fremstaa i Landet). Han tager sig ikke af det bortkomne, leder ikke efter det vildfarne, læger ikke det brudte og har ikke Omhu for det sunde, men spiser Kødet af de fede Dyr og river Klovene af dem.
17 “Kaito ga banzan makiyayin nan, wanda ya bar garken! Bari takobi yă sare hannunsa da idonsa na dama! Bari hannunsa yă shanye gaba ƙaf, idonsa na dama kuma yă makance sarai!”
Ve, min Daare af en Hyrde, som svigter Faarene! Et Sværd imod hans Arm og hans højre Øje! Hans Arm skal vorde vissen, hans højre Øje blindes.

< Zakariya 11 >