< Zakariya 10 >

1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Pedido de chuva de Yahweh na primavera, Yahweh que faz nuvens de tempestade, e ele dá chuveiros de chuva a todos para as plantas no campo.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
Pois os teraphim falaram vaidade, e os adivinhadores viram uma mentira; e eles contaram sonhos falsos. Confortam em vão. Portanto, eles seguem seu caminho como ovelhas. Eles são oprimidos, porque não há pastor.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
Minha raiva é acesa contra os pastores, e castigarei os caprinos machos, pois Javé dos Exércitos visitou seu rebanho, a casa de Judá, e os fará como seu majestoso cavalo na batalha.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
dele virá a pedra angular, dele a cavilha da barraca, dele, o arco de batalha, dele todos os governantes juntos.
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
Eles serão homens tão poderosos, pisando em ruas lamacentas na batalha. Eles vão lutar, porque Yahweh está com eles. Os cavaleiros a cavalo ficarão confusos.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
“Vou fortalecer a casa de Judá, e eu salvarei a casa de José. Eu os trarei de volta, pois eu tenho piedade deles. Eles serão como se eu não os tivesse jogado fora, pois eu sou Yahweh seu Deus, e eu os ouvirei.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
Ephraim será como um homem poderoso, e seu coração se regozijará como pelo vinho. Sim, seus filhos o verão e se regozijarão. Seu coração ficará contente em Yahweh.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
Eu farei sinal para eles e os recolherei, pois eu os resgatei. Eles vão aumentar como antes.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
Semeá-las-ei entre os povos. Eles vão se lembrar de mim em países distantes. Eles viverão com seus filhos e voltarão.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
Vou trazê-los novamente também para fora da terra do Egito, e os recolhe fora da Assíria. Vou trazê-los para a terra de Gilead e do Líbano; e não haverá espaço suficiente para eles.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
Ele passará pelo mar da aflição, e atingirá as ondas no mar, e todas as profundezas do Nilo secarão; e o orgulho da Assíria será derrubado, e o cetro do Egito irá partir.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
Vou fortalecê-los em Yahweh. Eles andarão para cima e para baixo em seu nome”, diz Yahweh.

< Zakariya 10 >