< Zakariya 10 >
1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Pedi ao Senhor chuva no tempo da serodia: o Senhor faz relâmpagos, e lhes dará chuveiro de água, e erva no campo a cada um.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
Porque os teraphins tem falado vaidade, e os adivinhos tem visto mentira, e falam sonhos vãos; com vaidade consolam, por isso se foram como ovelhas, foram aflitos, porque não havia pastor.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
Contra os pastores se acendeu a minha ira, e visitarei os bodes; mas o Senhor dos exércitos visitará o seu rebanho, a casa de Judá, e os fará ser como o cavalo da sua magestade na peleja.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
Dele a pedra de esquina, dele a estaca, dele o arco de guerra, dele juntamente sairão todos os exatores.
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
E serão como valentes que pelo lodo das ruas entram na peleja, e pelejarão; porque o Senhor estará com eles, e envergonharão aos que andam montados em cavalos.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
E fortalecerei a casa de Judá, e salvarei a casa de José, e tornarei a planta-los, porque me apiedei deles: e serão como se os não tivera rejeitado; porque eu sou o Senhor seu Deus, e os ouvirei.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
E os de Ephraim serão como um valente, e o seu coração se alegrará como de vinho, e seus filhos o verão, e se alegrarão; o seu coração se regozijará no Senhor.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
Eu lhes assobiarei, e os ajuntarei, porque eu os tenho remido, e multiplicar-se-ão, assim como antes se tinham multiplicado.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
E eu os semearei por entre os povos, e lembrar-se-ão de mim em lugares remotos; e viverão com seus filhos, e voltarão.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
Porque eu os farei voltar da terra do Egito, e os congregarei da Assyria; e tra-los-ei à terra de Gilead e do líbano, e não se achará lugar para eles.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
E ele passará o mar com angústia, e ferirá as ondas no mar, e todas as profundezas dos rios se secarão: então será derribada a soberba da Assyria, e o cetro do Egito se retirará.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
E eu os fortalecerei no Senhor, e andarão no seu nome, diz o Senhor.