< Zakariya 10 >

1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
باران را در موسم باران آخر از خداوندبطلبید. از خداوند که برقها را می‌سازدو او به ایشان باران فراوان هرکس در زمینش گیاه خواهد بخشید.۱
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
زیرا که ترافیم سخن باطل می‌گویند و فالگیران رویاهای دروغ می‌بینند وخوابهای باطل بیان می‌کنند و تسلی بیهوده می‌دهند، از این جهت مثل گوسفندان آواره می‌باشند و از نبودن شبان ذلیل می‌گردند.۲
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
خشم من بر شبانان مشتعل شده است و به بزهای نرعقوبت خواهم رسانید زیرا که یهوه صبایوت ازگله خود یعنی از خاندان یهودا تفقد خواهد نمودو ایشان را مثل اسب جنگی جلال خود خواهدگردانید.۳
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
از او سنگ زاویه و از او میخ و از اوکمان جنگی و از او همه ستمکاران با هم بیرون می‌آیند.۴
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
و ایشان مثل جباران (دشمنان خود را)در گل کوچه‌ها در عرصه جنگ پایمال خواهندکرد و محاربه خواهند نمود زیرا خداوند با ایشان است و اسب‌سواران خجل خواهند گردید.۵
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
و من خاندان یهودا را تقویت خواهم کرد وخاندان یوسف را خواهم رهانید و ایشان را به امنیت ساکن خواهم گردانید، زیرا که بر ایشان رحمت دارم و چنان خواهند بود که گویا ایشان راترک ننموده بودم زیرا یهوه خدای ایشان من هستم؛ پس ایشان را اجابت خواهم نمود.۶
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
وبنی افرایم مثل جباران شده، دل ایشان گویا ازشراب مسرور خواهد شد و پسران ایشان چون این را بینند شادی خواهند نمود و دل ایشان در خداوند وجد خواهد کرد.۷
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
و ایشان را صدا زده، جمع خواهم کرد زیرا که ایشان را فدیه داده‌ام وافزوده خواهند شد چنانکه در قبل افزوده شده بودند.۸
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
و ایشان را در میان قوم‌ها خواهم کاشت ومرا در مکان های بعید بیاد خواهند‌آورد و باپسران خود زیست نموده، مراجعت خواهندکرد.۹
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
و ایشان را از زمین مصر باز خواهم آورد واز اشور جمع خواهم نمود و به زمین جلعاد ولبنان داخل خواهم ساخت و آن گنجایش ایشان را نخواهد داشت.۱۰
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
و او از دریای مصیبت عبورنموده، امواج دریا را خواهد زد و همه ژرفیهای نهر خشک خواهد شد و حشمت اشور زایل خواهد گردید و عصای مصر نیست خواهد شد.۱۱
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
و ایشان را در خداوند قوی خواهم ساخت ودر نام او سالک خواهند شد. قول خداوند این است.۱۲

< Zakariya 10 >