< Zakariya 10 >

1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Bed Herren om regn når tiden for vårregnet er inne! Herren sender lynstråler, og regnskyll skal han gi dem, så hver mann får grøde på sin mark.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
For husgudene talte usant, og spåmennene skuet løgn; tomme drømmer forkynte de, og den trøst de gav, var intet verd; derfor måtte folket dra avsted som får og li ondt, fordi der ingen hyrde var.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
Mot hyrdene er min vrede optendt, og bukkene vil jeg hjemsøke; for Herren, hærskarenes Gud, ser til sin hjord, Judas hus, og gjør den lik sin stolte stridshest.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
Fra det skal hjørnestenene komme, fra det naglene, fra det krigsbuene - fra det skal alle herskere utgå.
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
Og de skal være lik kjemper som trår sine fiender ned i krigen likesom skarnet på gatene; ja, stride skal de, for Herren er med dem, og de som rider på hester, skal bli til skamme.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
Jeg vil styrke Judas hus og frelse Josefs hus og gi dem et bosted; for jeg forbarmer mig over dem, og de skal være som om jeg aldri hadde forkastet dem; for jeg er Herren deres Gud og vil bønnhøre dem.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
Og Efra'ims menn skal være lik kjemper, og deres hjerter skal bli glade som av vin; deres barn skal se det og glede sig, deres hjerter skal fryde sig i Herren.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
Jeg vil pipe til dem og samle dem, for jeg har utfridd dem; og de skal bli tallrike, som de har vært.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
Og jeg vil så dem ut blandt folkene, men i de fjerne land skal de komme mig i hu; og de skal leve med sine barn og komme tilbake.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
Og jeg vil føre dem tilbake fra Egyptens land og samle dem fra Assur og føre dem til Gileads land og til Libanon, og der skal det ikke bli rum nok for dem.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
Han skal dra frem gjennem havet, gjennem farer, og slå ned bølgene i havet, og alle Nilens dyp skal tørkes ut, og Assurs stolthet skal støtes ned, og kongespiret skal vike fra Egypten.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
Jeg vil gjøre dem sterke i Herren, og i hans navn skal de gå frem, sier Herren.

< Zakariya 10 >