< Zakariya 10 >

1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Jika musim semi tiba, mintalah hujan kepada TUHAN. Maka TUHAN akan mengumpulkan awan mendung, dan menurunkan hujan lebat sehingga ladang-ladang menjadi hijau dan segar bagi semua orang.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
Orang-orang minta petunjuk kepada berhala-berhala dan para peramal, tetapi jawaban-jawaban yang mereka dapat adalah dusta serta omong kosong belaka. Ada yang menerangkan mimpi, tetapi keterangan mereka hanya menyesatkan kamu, dan hiburan yang diberikannya tak ada artinya. Sebab itu rakyat tercerai-berai seperti domba. Mereka merana karena tidak punya pemimpin.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
TUHAN berkata, "Aku marah sekali kepada penguasa yang memerintah umat-Ku, dan mereka akan Kuhukum. Tetapi penduduk Yehuda adalah milik-Ku, dan Aku, TUHAN Yang Mahakuasa akan memelihara mereka. Mereka akan Kujadikan kuda perang yang perkasa bagi-Ku.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
Dari antara mereka akan Kupilih penguasa, pemimpin, dan panglima yang akan memerintah umat-Ku."
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
Penduduk Yehuda akan menang seperti pejuang-pejuang yang menginjak-injak musuh bagai lumpur di jalanan. Mereka akan berjuang karena Aku, TUHAN membantu mereka, dan pasukan musuh yang menunggang kuda akan mereka kalahkan semua.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
"Penduduk Yehuda akan Kukuatkan, umat Israel akan Kuselamatkan. Kubawa mereka kembali ke negerinya karena Aku sayang kepada mereka. Akan Kuperlakukan mereka seperti bangsa yang tak pernah Kuingkari. Akulah TUHAN Allah mereka, segala doanya akan Kuperhatikan lagi.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
Umat Israel akan seperti pahlawan yang kuat, seperti orang yang minum anggur, mereka akan gembira. Keturunan mereka dari zaman ke zaman tak akan melupakan kemenangan ini yang Kuberikan. Mereka akan bersukacita karena perbuatan-Ku bagi mereka.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
Umat-Ku akan Kupanggil dan Kukumpulkan menjadi satu. Mereka Kubebaskan dan Kubuat sebanyak dahulu.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
Meskipun Kusebar mereka ke tengah bangsa-bangsa, mereka akan tetap mengingat Aku di sana. Mereka akan selamat, begitu juga anak-anaknya dan akan pulang bersama-sama ke negerinya.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
Dari Mesir dan Asyur, mereka akan Kupulangkan. Di negerinya sendiri mereka akan Kutempatkan. Kubawa mereka ke Gilead dan Libanon juga, sehingga seluruh negeri penuh dengan mereka.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
Bila mereka menyeberangi lautan kesukaran, Aku, TUHAN akan memukul gelombang-gelombang; maka dasar Sungai Nil menjadi kering kerontang. Bangsa Asyur yang sombong akan direndahkan, dan Mesir yang perkasa akan kehilangan kekuasaan.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
Aku akan menguatkan umat-Ku, mereka akan taat dan berbakti kepada-Ku. Aku, TUHAN, telah berbicara."

< Zakariya 10 >