< Zakariya 10 >

1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Demandez à l'Éternel la pluie, au temps des pluies de l'arrière-saison. L'Éternel produira des éclairs; il vous donnera une pluie abondante et à chacun de l'herbe dans son champ.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
Car les théraphim ont parlé faussement, et les devins ont vu le mensonge; ils profèrent des songes vains et donnent des consolations de néant. C'est pourquoi ils s'en vont comme des brebis; ils sont misérables faute de berger.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
Ma colère s'est enflammée contre les bergers, et je punirai les boucs; car l'Éternel des armées visite son troupeau, la maison de Juda, et il en fait comme son cheval d'honneur dans la bataille.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
De lui vient la pierre angulaire, de lui le pieu de la tente, de lui l'arc de combat; de lui sortiront tous les chefs ensemble.
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
Ils seront comme de vaillants hommes foulant la boue des rues dans la bataille; ils combattront, car l'Éternel est avec eux, et les cavaliers sur leurs chevaux seront confondus.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
Je fortifierai la maison de Juda; je sauverai la maison de Joseph; et je les rétablirai, car j'ai compassion d'eux; et ils seront comme si je ne les avais pas rejetés; car je suis l'Éternel leur Dieu, et je les exaucerai.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
Et Éphraïm sera comme un héros; leur cœur sera joyeux comme par le vin; leurs fils le verront, et se réjouiront; leur cœur s'égaiera en l'Éternel.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
Je sifflerai vers eux, et je les rassemblerai, car je les rachète; et ils seront nombreux comme ils l'ont été.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
Je les ai disséminés parmi les peuples, mais dans les pays éloignés ils se souviendront de moi; et ils vivront avec leurs enfants, et ils reviendront.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
Je les ramènerai du pays d'Égypte, et je les rassemblerai de l'Assyrie; je les ferai venir au pays de Galaad et au Liban, et il n'y aura pas assez de place pour eux.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
Il passera la mer étroite, et frappera les flots de la mer; et toutes les profondeurs du fleuve seront desséchées; l'orgueil de l'Assyrie sera abattu, et le sceptre de l'Égypte sera ôté.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
Je les fortifierai en l'Éternel, et ils marcheront en son nom, dit l'Éternel.

< Zakariya 10 >