< Zakariya 10 >
1 Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
Ask ye of Jehovah rain in the time of the latter rain! It is Jehovah that maketh the lightning; And he will give you abundant showers, To every one the herb of the field.
2 Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
For the teraphim speak falsehood, And the diviners see a lie, And the dreams speak falsehood; Vain are their consolations. Therefore they wander as a flock; They are in distress, because there is no shepherd.
3 “Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
My anger is kindled against the shepherds, And the bucks will I punish; For Jehovah of hosts will visit his flock, the house of Judah, And make them as his goodly horse in battle.
4 Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
From him shall come forth the corner-stone, From him the nail, From him the battle-bow; From him shall every leader come forth.
5 Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
And they shall be as mighty men, Who tread down their enemies in battle as the mire of the streets, And they shall fight, because Jehovah is with them, So that the riders on horses shall be confounded.
6 “Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
And I will strengthen the house of Judah, And give victory to the house of Joseph, And I will set them in their dwellings, because I have compassion upon them; And they shall be as though I had not cast them off; For I am Jehovah, their God, and I will hear them.
7 Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
And Ephraim shall be as a mighty man, And their heart shall rejoice, as through wine; And their sons shall see it and rejoice, Their hearts shall rejoice in Jehovah.
8 Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
I will whistle for them, and will gather them; for I have redeemed them; And they shall increase as they increased before.
9 Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
Though I scatter them among the nations, Yet in far countries will they remember me; And they shall live with their children, and shall return.
10 Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
And I will bring them back from the land of Egypt, And from Assyria will I gather them; And I will bring them into the land of Gilead and of Lebanon, And there shall not be room enough for them.
11 Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
And he shall pass through the sea of distress, And he shall smite the sea of waves, And all the depths of the river shall be dried up; And the pride of Assyria shall be brought down, And the sceptre of Egypt shall depart.
12 Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.
And I will strengthen them through Jehovah, And in his name shall they walk, saith Jehovah.