< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
I åttonde månaden av Darejaves' andra regeringsår kom HERRENS ord till Sakarja, son till Berekja, son till Iddo, profeten, han sade:
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
Svårt förtörnad var HERREN på edra fäder.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Säg därför nu till folket så säger HERREN Sebaot: Vänden om till mig, säger HERREN Sebaot, så vill jag vända om till eder, säger HERREN Sebaot.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Varen icke såsom edra fäder, för vilka forna tiders profeter predikade och sade: "Så säger HERREN Sebaot: Vänden om från edra onda vägar och edra onda gärningar"; men de ville icke höra och aktade icke på mig säger HERREN.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Edra fäder, var äro de? Och profeterna, leva de kvar evinnerligen?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
Nej, men mina ord och mina rådslut, de som jag betrodde åt mina tjänare profeterna, de träffade ju edra fäder, så att de måste vända om och säga: "Såsom HERREN Sebaot hade beslutit att göra med oss, och såsom våra vägar och våra gärningar förtjänade, så har han ock gjort med oss."
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
På tjugufjärde dagen i elfte månaden, det är månaden Sebat, i Darejeves' andra regeringsår, kom HERRENS ord till Sakarja, son till Berekja, son till Iddo, profeten; han sade:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
Jag hade en syn om natten: Jag fick se en man som red på en röd häst; och han höll stilla bland myrtenträden i dalsänkningen. Och bakom honom stodo andra hästar, röda, bruna och vita.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
Då frågade jag: "Vad betyda dessa, min herre?" Ängeln som talade med mig svarade mig: "Jag vill låta dig förstå vad dessa betyda."
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
Och mannen som stod bland myrtenträden tog till orda och sade: "Det är dessa som HERREN har sänt ut till att fara omkring på jorden."
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
Och själva togo de till orda och sade till HERRENS ängel, som stod bland myrtenträden: "Vi hava farit omkring på jorden och hava funnit hela jorden lugn och stilla."
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Då tog HERRENS ängel åter till orda och sade: "HERRE Sebaot, huru länge skall det dröja, innan du förbarmar dig över Jerusalem och Juda städer? Du har ju nu varit vred på dem i sjuttio år."
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
Och HERREN svarade ängeln som talade med mig goda och tröstliga ord;
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
och ängeln som talade med mig sade sedan till mig: "Predika och säg: Så säger HERREN Sebaot: Jag har stor nitälskan för Jerusalem och Sion;
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
och jag är storligen förtörnad på hednafolken, som sitta så säkra; ty när jag var allenast litet förtörnad, hjälpte de ytterligare till att fördärva.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Därför säger HERREN så: Jag vill åter vända mig till Jerusalem i barmhärtighet; mitt hus skall där bliva uppbyggt, säger HERREN Sebaot, och mätsnöret skall spännas över Jerusalem.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Ytterligare må du predika och säga: Så säger HERREN Sebaot: Ännu en gång skola mina städer få njuta överflöd av goda håvor; ja, HERREN skall ännu en gång trösta Sion, och ännu en gång skall han utvälja Jerusalem."
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
Sedan lyfte jag upp mina ögon och fick då se fyra horn.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
Då frågade jag ängeln som talade med mig: "Vad betyda dessa?" Han svarade mig: "Detta är de horn som hava förstrött Juda, Israel och Jerusalem."
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
Sedan lät HERREN mig se fyra smeder.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
Då frågade jag: "I vad ärende hava dessa kommit?" Han svarade: "De förra voro de horn som förströdde Juda, så att ingen kunde upplyfta sitt huvud; men nu hava dessa kommit för att injaga skräck hos dem, och för att slå av hornen på de hednafolk som hava lyft sitt horn mot Juda land, till att förströ dess inbyggare."

< Zakariya 1 >