< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
I den åttende måned i Darius' annet år kom Herrens ord til profeten Sakarias, sønn av Berekias, sønn av Iddo, og det lød så:
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
Stor var Herrens vrede mot eders fedre.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Og du skal si til dem: Så sier Herren, hærskarenes Gud: Vend om til mig, sier Herren, hærskarenes Gud, så vil jeg vende om til eder, sier Herren, hærskarenes Gud.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Vær ikke lik eders fedre, som de forrige profeter formante med disse ord: Så sier Herren, hærskarenes Gud: Vend om fra eders onde veier og eders onde gjerninger! Men de hørte ikke og aktet ikke på mig, sier Herren.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Eders fedre, hvor er de? Og profetene, kan de leve til evig tid?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
Men mine ord og mine råd, som jeg bød mine tjenere profetene å forkynne, har ikke de nådd eders fedre, så de vendte om og sa: Som Herren, hærskarenes Gud, hadde i sinne å gjøre med oss efter våre veier og våre gjerninger, således har han gjort med oss?
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
På den fire og tyvende dag i den ellevte måned, det er måneden sebat, i Darius' annet år, kom Herrens ord til profeten Sakarias, sønn av Berekias, sønn av Iddo, og det lød så:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
Jeg hadde et syn om natten: Jeg så en mann som red på en rød hest, og han holdt stille blandt myrtetrærne i dalbunnen; og bak ham var det røde, blakke og hvite hester.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
Da sa jeg: Hvad er dette, herre? Og engelen som talte med mig, sa til mig: Jeg vil la dig se hvad dette er.
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
Da tok mannen som holdt stille blandt myrtetrærne, til orde og sa: Dette er de som Herren har sendt ut for å fare omkring på jorden.
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
Og de svarte Herrens engel, som holdt stille blandt myrtetrærne, og sa: Vi har faret omkring på jorden og sett at hele jorden er rolig og stille.
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Da tok Herrens engel til orde og sa: Herre, hærskarenes Gud! Hvor lenge skal det vare før du forbarmer dig over Jerusalem og Judas byer, som du har vært vred på nu i sytti år?
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
Og Herren svarte engelen som talte med mig, gode og trøstefulle ord.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
Og engelen som talte med mig, sa til mig: Rop ut disse ord: Så sier Herren, hærskarenes Gud: Jeg er såre nidkjær for Jerusalem og Sion,
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
og såre vred er jeg på de trygge hedningefolk; for jeg var bare litt vred, men de hjalp med til ulykken.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Derfor sier Herren så: Jeg vender mig atter til Jerusalem med miskunnhet; mitt hus skal bygges der, sier Herren, hærskarenes Gud, og målesnoren skal strekkes ut over Jerusalem.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Rop atter og si: Så sier Herren, hærskarenes Gud: Ennu en gang skal mine byer flyte over av det som godt er, og Herren skal ennu en gang trøste Sion og ennu en gang utvelge Jerusalem.
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
Og jeg løftet mine øine op og fikk se fire horn.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
Da spurte jeg engelen som talte med mig: Hvad er dette? Og han sa til mig: Dette er de horn som har adspredt Juda, Israel og Jerusalem.
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
Så lot Herren mig se fire smeder.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
Da spurte jeg: Hvad kommer disse her for? Han svarte: Hornene har adspredt Juda, således at ingen vågde å løfte sitt hode, og nu er disse kommet for å forferde dem og slå av hornene på de hedningefolk som har løftet horn mot Juda land for å adsprede det.

< Zakariya 1 >