< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
Kahdeksantena kuukautena toisena Dariuksen vuotena, tapahtui Herran sana Sakarjalle Berekian pojalle, Iddon pojalle, prophetalle, sanoen:
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
Herra on ollut vihainen teidän isillenne sangen kovasti.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Sano siis heille: näin sanoo Herra Zebaot: kääntykäät minun tyköni, sanoo Herra Zebaot; niin minä käännyn teidän tykönne, sanoo Herra Zebaot.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Älkäät olko niinkuin teidän isänne, joille entiset prophetat saarnasivat, sanoen: näin sanoo Herra Zebaot: palatkaat teidän pahoista teistänne ja teidän häijystä menostanne; mutta ei he kuulleet, eikä totelleet minua, sanoo Herra.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Kussa nyt ovat teidän isänne? ja vieläkö prophetat elävät?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
Eikö niin ole tapahtunut, että minun sanani ja oikeuteni, jotka minä minun palveliaini prophetain kautta käskin, ovat teidän isiinne sattuneet? että heidän täytyi palata ja sanoa: niinkuin Herra Zebaot ajatteli meille tehdä meidän teittemme ja töittemme jälkeen, niin hän on myös meille tehnyt.
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
Neljäntenä päivänä kolmattakymmentä ensimäisessä kuukaudessa toistakymmentä, joka on Sebatin kuu, toisena Dariuksen vuotena, tapahtui Herran sana Sakarjalle Berekian pojalle, Iddon pojalle, prophetalle, ja hän sanoi:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
Minä näin yöllä, ja katso, mies istui ruskian hevosen päällä, ja seisahti myrttien sekaan laaksossa, ja hänen takanansa olivat ruskiat ja maksankarvaiset ja valkiat hevoset.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
Ja minä sanoin: minun herrani, kutka nämät ovat? Ja enkeli, joka minun kanssani puhui, sanoi minulle: minä osoitan sinulle, kutka nämät ovat.
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
Ja mies, joka myrttien seassa oli, vastasi ja sanoi: nämät ovat ne, jotka Herra on lähettänyt vaeltamaan lävitse maan.
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
Mutta he vastasivat Herran enkelille, joka myrttien seassa oli, ja sanoivat: me olemme vaeltaneet maan lävitse, ja katso, kaikki maa istuu alallansa.
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Niin vastasi Herran enkeli ja sanoi: Herra Zebaot, kuinka kauvan et sinä tahdo armahtaa Jerusalemia, ja Juudan kaupungeita, joille vihainen olet ollut nyt seitsemänkymmentä ajastaikaa?
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
Ja Herra vastasi sille enkelille, joka minun kanssani puhui, hyvillä ja lohdullisilla sanoilla.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
Ja enkeli, joka minua puhutteli, sanoi minulle: saarnaa ja sano: näin sanoo Herra Zebaot: minä olen suuresti kiivastunut Jerusalemille ja Zionille;
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
Mutta minä olen juuri vihainen myös suruttomille pakanoille; sillä minä olin ainoasti vähän vihainen, mutta he auttivat hävitykseen.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Sentähden näin sanoo Herra: minä palajan Jerusalemiin laupiudella, ja minun huoneeni pitää hänessä rakennettaman, sanoo Herra Zebaot; ja Jerusalemin päälle pitää mittanuora vedettämän.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Ja saarnaa vielä ja sano: näin sanoo Herra Zebaot: taas pitää minun kaupungeilleni hyvin käymän, ja Herra on Zionia taas lohduttava, ja Jerusalem taas valitaan.
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
Ja minä nostin silmäni ja näin: ja katso, siellä oli neljä sarvea.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
Ja minä sanoin enkelille, joka puhui minun kanssani: mitä nämät ovat? Hän sanoi minulle: nämät ovat ne sarvet, jotka Juudan, Israelin ja Jerusalemin hajoittaneet ovat.
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
Ja Herra osoitti minulle neljä seppää.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
Silloin minä sanoin: mitä ne tahtovat tehdä? Hän sanoi: ne ovat ne sarvet, jotka Juudan hajoittaneet ovat, juuri niin, ettei kenkään ole voinut päätänsä nostaa; nämät ovat tulleet niitä karkottamaan, ja lohkaisemaan pakanain sarvia, jotka Juudan maan ylitse sarven nostaneet ovat sitä hajoittaaksensa.

< Zakariya 1 >