< Titus 1 >
1 Bulus, bawan Allah da kuma manzon Yesu Kiristi saboda bangaskiyar zaɓaɓɓu na Allah da kuma sanin gaskiya wadda take kaiwa ga rayuwa ta tsoron Allah
Paul, a bondservant of God and an Apostle of Jesus Christ for building up the faith of God's own people and spreading a full knowledge of the truths of religion,
2 duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, (aiōnios )
in hope of the Life of the Ages which God, who is never false to His word, promised before the commencement of the Ages. (aiōnios )
3 da lokacin da Allah ya zaɓa ya cika sai ya bayyana maganarsa a sarari ta wurin wa’azin da aka danƙa mini amana ta wurin umarnin Allah Mai Cetonmu,
And at the appointed time He clearly made known His Message in the preaching with which I was entrusted by the command of God our Saviour:
4 Zuwa ga Titus, ɗana na gaske a tarayyarmu cikin bangaskiya. Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Kiristi Yesu Mai Cetonmu, su kasance tare da kai.
To Titus my own true child in our common faith. May grace and peace be granted to you from God the Father and Christ Jesus our Saviour.
5 Dalilin da ya sa na bar ka a Kirit shi ne don ka daidaita abubuwan da suka rage da ba a kammala ba, ka kuma naɗa dattawa a kowane gari, yadda na umarce ka.
I have left you behind in Crete in order that you may set right the things which still require attention, and appoint Elders in every town, as I directed you to do;
6 Dole dattijo yă kasance marar aibi, mijin mace guda, mutumin da’ya’yansa masu bi ne, waɗanda kuma ba a san su da lalata ko rashin biyayya ba.
wherever there is a man of blameless life, true to his one wife, having children who are themselves believers and are free from every reproach of profligacy or of stubborn self-will.
7 Da yake an danƙa wa mai kula da ikkilisiya riƙon amana saboda Allah, dole yă zama marar aibi ba mai girman kai ba, ba mai saurin fushi ba, ba mai buguwa ba, ba mai rikici ba, ba kuma mai son ƙazamar riba ba.
For, as God's steward, a minister must be of blameless life, not over-fond of having his own way, not a man of a passionate temper nor a hard drinker, not given to blows nor greedy of gain,
8 A maimakon haka dole yă zama mai karɓan baƙi, mai son abu nagari, mai kamunkai, mai adalci, mai tsarki da kuma natsattse.
but hospitable to strangers, a lover of goodness, sober-minded, upright, saintly, self-controlled;
9 Dole yă riƙe tabbataccen saƙon nan kam-kam yadda aka koyar, don yă iya ƙarfafa waɗansu da sahihiyar koyarwa yă kuma ƙaryata waɗanda suke gāba da shi.
holding fast to the faithful Message which he has received, so that he may be well qualified both to encourage others with sound teaching and to reply successfully to opponents.
10 Gama akwai’yan tawaye da yawa, masu surutun banza da masu ruɗi, musamman ƙungiyar masu kaciya.
For there are many that spurn authority--idle, talkative and deceitful persons, who, for the most part, are adherents of the Circumcision.
11 Dole a hana su yin magana, domin suna kawo rushewar iyalai ta wurin koyar da abubuwan da bai kamata su koyar ba don neman ƙazamar riba.
You must stop the mouths of such men, for they overthrow the faith of whole families, teaching what they ought not, just for the sake of making money.
12 Wani daga cikin annabawansu ma ya ce, “Kiretawa a kullum maƙaryata ne, mugayen dabbobi, ragwaye haɗamammu.”
One of their own number--a Prophet who is a countryman of theirs--has said, "Cretans are always liars, dangerous animals, idle gluttons."
13 Wannan shaida gaskiya ce. Saboda haka, sai ka tsawata musu sosai, don su zama sahihai a wajen bangaskiya,
This testimony is true. Therefore sternly denounce them, that they may be robust in their faith,
14 ba za su kuma mai da hankalinsu ga tatsuniyoyin Yahudawa ko ga umarnan waɗanda suke ƙin gaskiya ba.
and not give attention to Jewish legends and the maxims of men who turn their backs on the truth.
15 Ga tsarkaka kuwa, kome mai tsarki ne, amma ga waɗanda suke marasa tsarki da kuma marasa ba da gaskiya, ba abin da yake da tsarki. Gaskiya dai, hankulansu da lamirinsu duk marasa tsarki ne.
To the pure everything is pure; but to the polluted and unbelieving nothing is pure, but on the contrary their very minds and consciences are polluted.
16 Sun ɗauka cewa sun san Allah, amma ta wurin ayyukansu suna mūsunsa. Sun zama abin ƙyama, marasa biyayya, ba su ma isa su yi aiki nagari ba.
They profess to know God; but in their actions they disown Him, and are detestable and disobedient men, and for any good work are utterly useless.