< Titus 1 >
1 Bulus, bawan Allah da kuma manzon Yesu Kiristi saboda bangaskiyar zaɓaɓɓu na Allah da kuma sanin gaskiya wadda take kaiwa ga rayuwa ta tsoron Allah
PAUL, a servant of God, and a legate of Jesus the Messiah; according to the faith of the elect of God, and the knowledge of the truth which is in the fear of God,
2 duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, (aiōnios )
concerning the hope of eternal life, which the veracious God promised before the times of the world; (aiōnios )
3 da lokacin da Allah ya zaɓa ya cika sai ya bayyana maganarsa a sarari ta wurin wa’azin da aka danƙa mini amana ta wurin umarnin Allah Mai Cetonmu,
and in due time he hath manifested his word, by means of our announcement, which was confided to me by the command of God our Life-giver;
4 Zuwa ga Titus, ɗana na gaske a tarayyarmu cikin bangaskiya. Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Kiristi Yesu Mai Cetonmu, su kasance tare da kai.
to Titus, a real son after the common faith: Grace and peace from God our Father, and from our Lord Jesus the Messiah, our Life-giver.
5 Dalilin da ya sa na bar ka a Kirit shi ne don ka daidaita abubuwan da suka rage da ba a kammala ba, ka kuma naɗa dattawa a kowane gari, yadda na umarce ka.
For this cause left I thee in Crete, that thou mightest regulate the things deficient, and establish elders in every city, as I directed thee:
6 Dole dattijo yă kasance marar aibi, mijin mace guda, mutumin da’ya’yansa masu bi ne, waɗanda kuma ba a san su da lalata ko rashin biyayya ba.
him who is blameless, who is the husband of one wife, and hath believing children, who are no revellers, nor ungovernable in sensuality.
7 Da yake an danƙa wa mai kula da ikkilisiya riƙon amana saboda Allah, dole yă zama marar aibi ba mai girman kai ba, ba mai saurin fushi ba, ba mai buguwa ba, ba mai rikici ba, ba kuma mai son ƙazamar riba ba.
For an elder ought to be blameless, as the steward of God; and not be self-willed, nor irascible, nor excessive in wine, nor with hands swift to strike, nor a lover of base gains.
8 A maimakon haka dole yă zama mai karɓan baƙi, mai son abu nagari, mai kamunkai, mai adalci, mai tsarki da kuma natsattse.
But he should be a lover of strangers, and a lover of good deeds, and be sober, upright, kind-hearted, and restraining himself from evil passions;
9 Dole yă riƙe tabbataccen saƙon nan kam-kam yadda aka koyar, don yă iya ƙarfafa waɗansu da sahihiyar koyarwa yă kuma ƙaryata waɗanda suke gāba da shi.
and studious of the doctrine of the word of faith, that he may be able by his wholesome teaching both to console, and to rebuke them that are contentious.
10 Gama akwai’yan tawaye da yawa, masu surutun banza da masu ruɗi, musamman ƙungiyar masu kaciya.
For many are unsubmissive, and their discourses vain; and they mislead the minds of people, especially such as are of the circumcision.
11 Dole a hana su yin magana, domin suna kawo rushewar iyalai ta wurin koyar da abubuwan da bai kamata su koyar ba don neman ƙazamar riba.
The mouth of these ought to be stopped: they corrupt many families; and they teach what they ought not, for the sake of base gains.
12 Wani daga cikin annabawansu ma ya ce, “Kiretawa a kullum maƙaryata ne, mugayen dabbobi, ragwaye haɗamammu.”
One of them, a prophet of their own, said, The Cretans are always mendacious, evil beasts, idle bellies.
13 Wannan shaida gaskiya ce. Saboda haka, sai ka tsawata musu sosai, don su zama sahihai a wajen bangaskiya,
And this testimony is true. Therefore chide them sharply; that they may be sound in the faith,
14 ba za su kuma mai da hankalinsu ga tatsuniyoyin Yahudawa ko ga umarnan waɗanda suke ƙin gaskiya ba.
and may not throw themselves into Jewish fables, and into the precepts of men who hate the truth.
15 Ga tsarkaka kuwa, kome mai tsarki ne, amma ga waɗanda suke marasa tsarki da kuma marasa ba da gaskiya, ba abin da yake da tsarki. Gaskiya dai, hankulansu da lamirinsu duk marasa tsarki ne.
For to the pure, every thing is pure; but to them who are defiled and unbelieving, nothing is pure; but their understanding is defiled, and their conscience.
16 Sun ɗauka cewa sun san Allah, amma ta wurin ayyukansu suna mūsunsa. Sun zama abin ƙyama, marasa biyayya, ba su ma isa su yi aiki nagari ba.
And they profess that they know God, but in their works they deny him; and they are odious, and disobedient, and to every good work reprobates.