< Titus 3 >

1 Ka tuna wa mutane su zama masu biyayya ga masu mulki da kuma hukumomi, su zama masu biyayya suna kuma a shirye su yi kowane abin da yake mai kyau,
Lizinong nani i ne ati bara anan tigo nin nanan tica tig, inunku vat.
2 kada su zama masu ɓata sunan kowa, su zama masu salama da kulawa, su kuma zama masu matuƙar tawali’u ga dukan mutane.
Na iwa firin umong b, na iwa su mayerdan ba na isun anit ti bau mine nin dursuzu nteltinu nati udu na ti vat
3 A wani lokaci can baya mu ma wawaye ne, marasa biyayya, aka ruɗe mu, sha’awace-sha’awace da kwaɗayi iri-iri suka daure mu, muka yi zaman ƙiyayya da kishi, aka ƙi mu, mu kuma muka ƙi juna.
Bara nani arik atibite nwa di sa ukpilzu nin salin nunku nat, tiwa cinu hem ti so acin kuna niyizi nin lanzun mman. Tiwa di nanyan likara linanzan nnin shina. Tiwa nari ati bite nin salin laun mmang.
4 Amma da alheri da kuma ƙaunar Allah Mai Cetonmu suka bayyana,
Bara na nshau kibinai Kutelle unan tucu bite nin son suu me udu kitin nit adaa.
5 sai ya cece mu, ba saboda abubuwan adalcin da muka aikata ba, sai dai saboda jinƙansa. Ya cece mu ta wurin wankan nan na sāke haihuwa da kuma sabuntawan nan ta Ruhu Mai Tsarki,
Awa tucu nari nnuzun maru upese nin lipesen Nfip mi la, na bara ni tawaa na tisuzu b, bara nani nkunekune mer.
6 wanda ya zubo mana a yalwace ta wurin Yesu Kiristi Mai Cetonmu,
Kutelle na ni nari Nfip me milau nanya Yesu kristi unan tucu bite.
7 wannan fa domin an kuɓutar da mu ne ta wurin alherinsa, don mu zama magāda masu begen ga rai madawwami. (aiōnios g166)
Awa suu nani tina see usortu nanya mbolu Kutell, ti da su anan lin gadu nlai sa ligang nin likara kibinai. (aiōnios g166)
8 Wannan magana tabbatacciya ce, ina kuma so ka nanata waɗannan abubuwa ƙwarai, domin waɗanda suka dogara ga Allah su himmantu ga aiki mai kyau. Waɗannan abubuwa suna da kyau sosai suna kuma da amfani ga kowane mutum.
Too ti pipinghe tinyinuwari. Ndi nin suu iliru nin likara kibinai bara ele imon, ara ale na uyinna nin Kutelle iceu nibinai mine nitwa ni cine naa ana ceu nbugn min. I le imone caun nin se ugb ardan bara anit vat.
9 Amma ka guji jayayyar banza da ƙididdigar asali da gardandami da faɗace-faɗace game da Doka, gama ba su da riba kuma aikin banza ne.
Bara nani sunan mayardan tilalalng tone nin piziru na kura nin fizu nibinai nnun bara uduk. I leli imone na icau ba nin salin nimong kitene.
10 Ka gargaɗe mutumin da yake kawo tsattsaguwa sau ɗaya, ka kuma gargaɗe shi sau na biyu. Bayan haka, kada wani abu yă haɗa ka da shi.
Nari ule na adin dasu nin kosu natii nanya mine iwa malu wunughe atuf urun sa tiba.
11 Ka dai san cewa irin mutumin nan ya taurare kuma mai zunubi ne; ya yanke wa kansa hukunci.
Nin yinu au umusin ntele amlu killau liti me nanya libau ti terd nin tizu kulapi nca nkul.
12 Da zarar na aika Artemas ko Tikikus zuwa wurinka, sai ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka zo wurina a Nikofolis, domin na yanke shawara in ci damina a can.
Dana iwa tuu Artamas sa Tychikus ku kiti mine tanmas idak kiti nighe in Nikopolis kikaa nan ina yinin in soo ku kubin tutuwui.
13 Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka taimaki Zenas lauyan nan da Afollos a hanyarsu ka kuma tabbata ba su rasa kome ba.
Tanmas ituu Zinas ku unan yiru ndoka. nin Apollo, nin nimong ile na idinin suwe.
14 Dole mutanenmu su koyi ba da kansu ga aikata abin da yake nagari, domin su iya biyan bukatunsu na yau da kullum kada kuma su yi rayuwar marar amfani.
Na amit bite masu nitwa nicine nanga na nima bizu ti bukata ti kpaikpai bara iwa so sa nitwa ba
15 Dukan waɗanda suke tare da ni suna gaishe ka. Ka gaggai mini da masoyanmu, masu bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku duka.
Vat nale na idi nin me idin lisu min. Lison ale na idi ni su bite nanya yinnu sa uyenu ubolu Kutelle soo nan ghin. usuo nani

< Titus 3 >