< Titus 2 >

1 Dole ka koyar da abin da yake bisa sahihiyar koyarwa.
Hianagi kagrama rempi huzmisanana, tamage kema hu'nesia ke'age (doctrine) huzamasmio.
2 Ka koya wa tsofaffin maza su kasance masu sauƙinkai, waɗanda suka cancanci girmamawa, masu kamunkai, sahihai wajen bangaskiya, da ƙauna da kuma jimiri.
Ranra vene'nea rempi huzamige'za, fru kefinti kea antemase'za ranke osu'za, knare zmavuzmava nehu'za, knare zamagu'zamagesa antahiho. Hankave zamentinti nehu'za vaheku zamesi nezmante'za, zamentintifina hanaveti'za maniho.
3 Haka ma, ka koya wa tsofaffin mata su zama masu bangirma cikin rayuwarsu, ba masu ɓata suna ko masu jarrabar shan giya ba, sai dai su zama masu koyar da abin da yake nagari.
Ana zanke hunka ranra a'ne rempi huzamige'za, mikaza hanafina Anumzamofo agorga mani'ne'za, vahe agenke osu' aka timo'a zamazeri havia osanige'za knare'za rempi huzamiho.
4 Sa’an nan za su iya su koya wa mata masu ƙuruciya su ƙaunaci mazansu da’ya’yansu,
Ana nehu'za zamagra zahufa a'ne nagara zamumro antesage'za, ve' zamine, mofavrezaminena zamesi zamantegahaze.
5 su kasance da kamunkai da kuma tsarki, masu aiki a gida, masu kirki da kuma masu biyayya ga mazansu, don kada wani yă rena maganar Allah.
Knare zamagu'zamagesa nentahi'za avusese hu'za mani'ne'za, vaheku vahaku nehu'za, nezamave agorga'a mani'nesage'za nege'za Anumzamofo nanekea huhaviza osugahaze.
6 Haka kuma, ka ƙarfafa samari su zama masu kamunkai.
Anahu kna hunka nehazave nagara zamumro antege'za, kegava hu'za maniho.
7 Cikin kowane abu ka zama musu misali mai kyau ta wurin aikata abin da yake nagari. A cikin koyarwarka ka nuna mutunci da ƙwazo
Hakare'zama hanampina knare avu'ava huzamio. Huzameri hanampina zokago vakago osunka tamage ke'age nehunka,
8 da kuma sahihanci cikin maganar da ba za a iya kushewa ba, domin masu gāba da kai su ji kunya, su kuma rasa wani mugun abin da za su faɗa game da mu.
tamage ke'age huzamasmigeno mago'mo'a huhaviza huoganteno. E'ina hanankeno aza'o huhaviza hugantesimo'a agzegu hugahie. Na'ankure zamagra havigema hurante zankura hakregahaze.
9 Ka koya wa bayi su yi wa iyayengijinsu biyayya cikin kowane abu, su yi ƙoƙari su gamshe su, kada su mayar musu da magana,
Hagi kazokzo eri'za vahera rempi huzamige'za mika'zama hanafina kva vahe'mokizmi zamagorga mani'ne'za zamazeri muse nehu'za, ke nona'a huozmante'za,
10 kada kuma su yi musu sata, sai dai su nuna za a iya amince da su sosai, don ta kowace hanya su sa koyarwa game da Allah Mai Cetonmu ta zama abin ɗaukan hankali.
mago'zazamia kumzafa oseho. Hagi eri'zana tamage kazigati erifatgo nehanageno, e'i anazamo Anumza tzahu ne'mofo mani'za huzamerisage'za nege'za, mono nontahisaza kva vahe'mo'zane, megi'a vahe'mo'za zamagu'a rukrahe hugahaze.
11 Gama alherin Allah mai kawo ceto ya bayyana ga dukan mutane.
Na'ankure Anumzamofo asunku zamo vahe avare'zana hakare vahete erino efore hu'ne.
12 Yana koya mana mu ce, “A’a” ga rashin tsoron Allah da kuma sha’awace-sha’awacen duniya, mu kuma yi rayuwa ta kamunkai, ta adalci da kuma ta tsoron Allah a cikin wannan zamani, (aiōn g165)
Tagri rempi huramino mono ontahi avu'ava'zane, ama mopafi zanku avesi'zanena atreho nehuno, hagi tamufa kva huta, fatgo huta Anumzamofo (godly) avu'avate ama kna'afina maniho. (aiōn g165)
13 yayinda muke sauraron begenmu mai albarka bayyanuwar ɗaukakar Allahnmu mai girma da kuma Mai Cetonmu, Yesu Kiristi,
Hagi ana knama esigu avega anteneta muse nehune, tusi'a masa'afi efore hanigu, Ra Anumzantima, Tazahu ne' Krais Jisasi esigu avega ante'none.
14 wanda ya ba da kansa dominmu don yă fanshe mu daga dukan mugunta yă kuma tsarkake wa kansa mutanen da suke nasa, waɗanda suke marmarin yin abin da yake nagari.
Tagriku huno Agra'a avufga atreno kefo'zampinti miza seranteno tvare atre'ne, Agri'a vahere huno sese huranteno, tvare Agrarega tante'negu, muse nehuta knare zanke hanune.
15 Waɗannan kam, su ne abubuwan da ya kamata ka koyar, ka ƙarfafa ka kuma tsawata da dukan iko. Kada ka yarda wani yă rena ka.
Mika'zana kagripi hampo'na huno me'neanki rempi hunezminka, hampo'na tinka nezmasaminka, zamazeri fatgo nehuge'za, kagrikura amne vahere hu'za osiho.

< Titus 2 >